Dawowar Sanusi II da London: Kano ta dauki dumi, kanawa sun mamaye filin jirgi


Legit Hausa

Jama'ar jihar Kano sun yi tururuwa zuwa filin tashi da saukar jirage na Mallam Aminu Kano domin tarbar mai martaba sarki Sanusi II wanda zai dawo ake saka ran saukar sa daga kasar Ingila.

Daruruwan mutanen Kano sun yi dafifi da yammacin ranar Lahadi zuwa filin jirgin domin nuna soyayyar su da kauna ga sarki Sanusi II bayan gwamnatin jihar Kano ta raba masarautar Kano zuwa gida biyar.

Ana rade-radin cewar za a iya samun hargitsi saboda wasu masu goyon bayan gwamnati sun shirya gudanar da yin gangamin nuna wa sarki Sanusi goyon bayan su a kan matakin da gwamnatin jihar Kano ta dauka.

Kazalika, an zargi jami'an 'yan sanda da hana dandazon jama'ar tarbar sarki Sanusi kuma tsohon gwamnan babban bankin kasa (CBN). Kwamishinan 'yan sandan jihar Kano, CP Mohammed Wakili, ya shiada wa majiyar mu cewar bai bayar da umarnin hana wasu jama'a gudanar da taron gangami ba, matukar sun yi hakan cikin lumana da zaman lafiya.

A ranar Laraba ne gwamna Ganduje ya rattaba hannu a kan dokar kirkirar sabbin masarautu hudu daga masarautar Kano. A ranar Asabar ne gwamnan ya rantsar da sabbin sarakunan yanka na masarautu hudun da aka kirkira. Sabbin masarautun su ne; Bichi, Gaya, Karaye da Rano. Ana saka ran sarki Sanusi zai sauka a Kano da misalin karfe 4:15 na yamma, kamar yadda majiyar fada ta sanar.

DAGA ISYAKU.COM 

Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews 

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM 

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN