Badakalar kudi: Kotun tarayya ta bayar da umarnin kama tsohon Gwamna Aliyu


Legit Hausa

Alkalin kotun tarayya da ke Minna, Jastis Aminu Aliyu, a ranar Alhamis 23 ga watan Mayu, ya bayar da umurnin kamo tsohon gwamnan Jihar Niger, Babangida Aliyu da Umar Nasko. 

Jastis Aliyu ya kume janye belin da Jastis Yellim Bogoro ya bawa Aliyu da Nasko saboda rashin bayyana a kotu domin cigaba da sauraron shari'ar da ake musu. Kamfanin dillancin labarai na kasa (NAN), ta ruwaito cewa kotu ta bukaci Aliyu da Nasko su gurfana a gabanta a ranar Alhamis ne domin sake fara sauraron shari'ar tuhumar da ake musu na damfarar Naira Biliyan 1.9 da aka mayar zuwa kotun Jastis Aliyu. Lauyansu shima bai bayyana a gaban kotu ba. Olajide 

Ayodele, lauyan Gwama Aliyu, ya aike wa kotu da wasika inda ya roki a dage cigaba da sauraron karar. Daga karshe an dage cigaba da sauraron karar zuwa ranar 27 ga watan Mayun 2019 kamar yadda NAN ta ruwaito
 

DAGA ISYAKU.COM

Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN