Legit Hausa
Gwamnan jihar Sokoto, Aminu Tambuwal, a jiya Lahadi, 19 ga
watan Mayu yayi zargin shirye shiryen haddasa rigingimun siyasa a jihar, kamar
yanda ya jaddada cewa babu wanda ya isa ya hana a rantsar da shi a ranar 29 ga
watan Mayu.
Yayin da yake magana ta hannun babban hadiminsa, Alhaji
Yusuf Dingyadi, gwamnan yayi zargin cewa wassu mutane suna yada karerayi da
kuma haddasa rudani cewa kotu tana shirin tsige shi daga kujerarsa sannan ta
mika mulkin ga APC.
Ya kara da cewa an cire fostan shi da aka lika a hanyar
Birnin Kebbi, hanyar tashar jirgi da Maiduguri an kuma mayar da fostan dan
takaran jam’iyyar APC. Tambuwal ya karfafa cewa kotu kadai ce take da karfin
hana gwamnatinsa.
Gwamnan ya shawarci jam’iyyar adawa da ta “bar kotu ta
gudanar da aikin ta, jam’iyyar PDP a Sokoto bata nemi hukunci ta kofar baya ba.
Kawai a bar kotu tayi abunda ya dace, muna da tabbaci akan kotu saboda mun
lashe zabe ne da ikon Allah.”
DAGA ISYAKU.COM
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Tags:
LABARI