Legit Hausa
Yayin da musulmai suka fara azumin
watan ramadana a ranar Litinin, jam’iyyar All Progressives Congress, (APC) ta
roki musulmai da su kiyayi malamai, don wannan lokacin ne ake amfani da shi
wajen yada kalaman kiyayya akan gwamnatin shugaban kasa Muhammadu Buhari.
Babban sakataren sadarwa na
jam’iyyar, Mallam Lanre Issa-Onilu ya bayyana gargadin a sakon watan ramadana
da ya gabatar ga manema labarai. Kakakin APC din ya shawarci yan Najeriya da su
kai rahoto ga hukumomi akan masu boyewa a karkashin inuwar malamta don gudanar
da mugun nufi ko neman boyan bukatunsu.
Mallam Onilu wanda ya amince a wani
jawabi cewa “lamarin garkuwa da mutane, ta’addanci, rikicin kabilu da na
addinai da rigingimu da sauran laifuffukan da ake daukakawa a wassu yankunan
kasar sun kasance abun damuwa matuka.
"Haka zalika ya yi ikirarin
cewa “gwamnatin shugaban kasa Muhammadu Buhari na dauke da matakai mai nau’i da
dama wajen ganin ta magance rigingimu sannan ya cigaba da bayyana cewa
“shugaban kasar ya bada umurni ga hukumomin tsaro masu muhimmanci da su yi
maganin duk wata barazana akan harkar tsaro, su kuma tabbatar da zaman lafiya a
yankunan da ke fuskantan tashin hankali.”
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi