An kashe mutum 50, an raunta 30 bayan an kai hare-hare a Zamfara


Legit Hausa

‘Yan bindiga sun hallaka Bayin Alla da-dama a wasu hare-hare har 3 da aka kai a cikin Garuruwan jihar Zamfara a karshen makon jiya. Jaridar Punch ta rahoto adadin mutanen da aka kashe a jihar. Akalla mutane 50 ne aka hallaka, bayan an ji wa wasu 31 rauni a cikin hare-haren da aka kai cikin Zamfara kwanan nan.

Wasu ‘Yan bindiga dai sun hana mutanen yankin Dangurgu, kunkilai, da Birnin Magaji sakat a cikin kwanakin nan. Hari 3 aka kai a cikin wadannan Garuruwa da ke cikin kananan hukumomin Maru, Gusau da kuma Birnin Magaji a karshen makon da ya gabata, Hakan na zuwa ne bayan jami’an tsaro sun yi azamar kawo karshen ta’adin da ake yi a jihar.

Dakarun ‘yan sanda sun kaddamar da wani shiri na ‘Operation Puff Adder’ da ake sa rai zai kawo karshen kashe mutanen da ake yi a Garuruwan Zamfara da kewaye. Amma sai ga shi an kashe mutum 50 a Ranar Asabar da ta wuce. Kamar yadda mu ka samu labari, wadannan ‘yan bindiga sun shiga Kauyen Kunkilai ne a Ranar 4 ga Watan Mayun nan inda su ka budawa wasu masu halartar bikin suna wuta.

A nan-take aka kashe mutane 30, kuma aka raunata mutum 6. A Ranar Juma’a kuma ‘Yan bindiga su ka kashe mutum 20 a Garin Magami da ke cikin Gusau, an kuma yi wa mutum 15 rauni a harin daga ciki har da sojoji. Jami’an tsaro sun tabbatar da aukuwar wannan hari bayan ‘yan bindigan sun tsere.

DAGA ISYAKU.COM

Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN