Legit Hausa
Hukumar hana ta'ammuli da fataucin
miyagun kwayoyi, NDLEA ta kama wani dattijo mai shekaru 72, Mohammed Hamza da
wani Kamisu Muhammad da haramtattun kwayoyi a filin tashi da saukan jirage na
kasa da kasa ta Mallam Aminu Kano (MAKIA). An damke dattijon ne yayin da ya ke
kokarin shiga jirgi zuwa kasar Saudiyya.
A yayin da ya ke yiwa manema labarai
jawabi a ranar Juma'a, Kwamandan NDLEA na MAKIA, Mr Ambrose Umoru ya ce an
kamane Hamza wanda dan asalin kauyen Gwaranduma ne a karamar hukumar Daura a
jihar Katsina a lokacin da ake bincikar kayayakin matafiya. Sai dai dattijon ya
shaidawa jami'an NDLEA cewa bai shi da masaniya a kan yadda akayi kwayoyin suka
shiga jakarsa.
"Mun gano cewa wasu ne da suka biya wa
dattijon kudin jirgi zuwa kasar Saudiyya suka saka kwayoyin Tramadol a cikin jakar
kayansa. Sun kawo shi Kano daga Katsina inda suka ajiye a Otel na kwanaki uku
kuma a wannan lokacin ne suka saka kwayoyin jikin jakarsa ba tare da saninsa
ba.
"A lokacin da jami'an mu suka
gano muggan kwayoyin kuma ya fada mana inda ya fito. Ba tare da bata lokaci ba
sai muka aike jami'an mu suka tsare Kamisu Mohammed. "Kamar yadda bayannan
mu suka nuna, an taba kama Mohammed da laifin saka muggan kwayoyi cikin
jakkunan wasu mata biyu a baya. Sai dai a wancan lokacin matan tare suke aiki
da Mohammed ba kamar dattijon nan da bai san hawa ba balle sauka," inji
Umoru.
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi