An bayyana kudin kujerun hajjin bana a Kaduna da Abuja


Legit Hausa

Jami'an yadda labarai na hukumomin, Malam Yunusa Abdullahi da Muhammad Lawal sun bayyana hakan ne a cikin sanarwar da suka fitar a Kaduna da Abuja. Sanarwar ta ce Cibiyar Kula da Aikin Hajji na Kasa ta amince da N1, 549,297.09 a matsayin kudin kujerar aikin hajji da kowane maniyyaci zai biya domin zuwa kasar Saudi Arabia sauke farali. 

Za kuma a bawa maniyyatan allawus din tafiya na $800.00. Abdullahi na jihar Kaduna ya ce mai sanya idanu kan hukumar Alhazai na jihar, Imam Hussaini Ikara ya yi bayyanin cewa an cimma matsaya a kan kudin ne bayan anyin lissafi da kudin masauki a Makkah da Madina da sauran abubuwa. "Ba a kayyade BTA ba kamar yadda akayi a shekarun baya. 

"Mutanen da suka gudanar da aikin hajji a shekaru hudu da suka gabata za su biya kari Riyal 2000 wanda ya yi daidai na N162.000." Sai dai Ikara ya shawarci maniyyata suyi gaggawan biyan kudin kejurun su domin tuni an fara aikin tantance biza kuma akwai bukatar a biya cikon kudin ga hukumar NAHCON kamar yadda aka tsara.
 

DAGA ISYAKU.COM

Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN