Legit
Hausa
Zirga-zirga
ta ragu a fadar Sarkin Kani, Muhammad Sanusi II, bayan kaddamar da sababbin
masarautun yanka guda hudu da gwamna Ganduje ya yi wanda suka hada da Bichi,
Rano, Karaye da kuma Gaya.
Ranar
Lahadin da ta gabata fadar a cike take da al'umma a lokacin da sarkin ya dawo
daga aikin Umrah, inda dubunnan mutane suka fito suna yi mishi barka da zuwa a
filin tashi da saukar jiragen sama na Malam Aminu Kano.
Mutanen
sun biyo shi har zuwa fadar shi daga filin jirgin, inda suke yi mishi kirarin
'Sarki Mai Martaba'. Mun samu labarin cewa a yau Talatar nan zirga-zirga ta
ragu sosai a fadar, duk yawan zirga-zirgar da aka saba gani a fadar ta mutane
da ababen hawa komai ya ragu.
Mutane
kalilan ne suka rage a fadar sai ma'aikatan fadar. Wani Dogari wanda ya yi
magana da manema labarai ya bukaci a boye sunansa, ya tabbatar da cewar sarkin
ya zabi ya kadaice kanshi tun dawowar shi daga kasa mai tsarki.
DAGA ISYAKU.COM
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Tags:
LABARI