Legit Hausa
Hukumomin kasar Saudiyya sun saki
Zainab Aliyu, matashiyar nan 'yan Najeriya da aka kama bisa zarginta da shiga
da kwaya kasar saudiyya.
A jawabin da babban sakatare a
ma'aikatar harkokin kasashen waje ta Najeriya ya fitar, ya ce yanzu haka Zainab
na ofishin jakadancin Najeriya dake kasar Saudiyya. Kazalika, ya bayyana cewa
hukumomin kasar Saudiyya za su saki Ibrahim Abubakar, wani dan Najeriya da ya
samu irin matsalar Zainab a kasar Saudiyya.
A ranar Litinin ne shugaban kasa
Muhammadu Buhari ya umarci ministan shari'a, Abubakar Malami, da ya tabbatar da
cewar hukumomin kasar Saudiyya sun saki matashiyar nan yar Najeriya, Zainab
Aliyu, da aka yi kuskuren kama wa bisa zargin laifin safarar kwaya.
Hukumomin kasar Saudiyya sun kama
Zainab, daliba a jami'ar Maitama Sule dake Kano, a ranar 26 ga watan Disamba na
shekarar 2018 bisa zarginta da shiga da jaka dauke da kwayar 'tramol' zuwa
kasar Saudiyya.
Matashiyar ta tashi zuwa kasar
Sauddiya daga filin jirgin sama na Mallam Aminu domin gudanar da aikin 'umra'
tare da mahaifiyarta, Maryam, da 'yar uwarta, Hajara. Babbar mai taimaka wa
shugaban kasa a bangaren harkokin da suka shafi kasashen waje, Abike Dabiri
Erewa, ce ta sanar da umarni da shugaba Buhari ya bayar a ranar Litinin, 29 ga
watan Afrilu, ta kara da cewa tuni gwamnatin tarayya ta fara tattauna batun
sakin Zainab tare da wasu mutane biyu dake da irin matsalar da Zainab ta samu.
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi