Legit Hausa
Wani babban Masanin harkar tattalin
arziki a Najeriya kuma shugaban kamfanin Dr Diran Fawibe a wata hira da yayi da
da jaridar Daily Trust yayi bayani a game da hako fetur da ake yi a Arewa.
Diran Fawibe ya bayyana cewa akwai bukatar a hako fetur din da ke Arewacin
Najeriya, Masanin yace wannan zai ba gwamnatin Najeriya kudin shiga, kuma zai
taimakawa masu kananan matatun danyen man fetur a cikin kasar.
Dr. Fawibe yake cewa ya kamata ace
Najeriya tayi nisa da fara aiki da man da ke kwance a Arewacin kasar kamar
yadda sauran kasashen Duniya su ke yi. Masanin ya dai nuna cewa hako man Arewa
zai taimaki Najeriya kwarai.
Bayan nan kuma wannan babban Masani
yace ana sa rai kamfanin tace danyen man fetur da Aliko Dangote yake ginawa ya
kammalu kwanan nan. Diran Fawibe yace samuwar wannan kamfani ba zai kashe
sauran matatun kasar ba.
Wannan kwararren Masanin ya nuna
cewa sha’anin tace man fetur yana da matukar wahala, har ya fi hako man fetur
zama jan-aiki. A wannan hira mai tsawo da yayi da ‘yan jarida, yace kayyade
farashin kayan mai bai da amfani. Shugaban kamfanin na International Energy
Services (IES), Fawibe, ya kuma bayyana cewa akwai bukatar shugaban kasa
Muhammadu Buhari ya sake duba kudirin nan na PIB da ake tunani zai gyara
sha’anin man fetur a Najeriya.
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi