Gwamnatin tarayya ta haramta hakar gwal a Zamfara

A daidai lokacin da kashe-kashe suka yi kamari a jihar Zamfara, gwamnatin Tarayya ta sanar da haramta duk wasu hidimomin hakar ma’adanai a fadin jihar Zamfara, sannan ta baiwa ‘yan kasashen wajen wa’adin sa’o’i 48 da su gaggauta ficewa daga yankunan da ake hakar ma’adanan. Mukaddashin Sufeto-Janar na ‘yan sandan Nijeriya, Muhammad Adamu ne ya fitar da wannan sanarwa yau Lahadi a fadar Shugaban Kasa a yayin da ya gana sa manema labarai, a cewarshi wannan yana daga cikin kokarinsu na kawo karshen barayin Zamfara. Babban jami’in ya bayyana hakan ne a daidai lokacin da suke tare da Shugaban Ma’aikatan fadar gwamnatin Tarayya, Abba Kyari, da darekta janar na hukumar DSS Yusuf Bichi, da kuma darekta janar na hukumar leken asiri ta Nijeriya wato NIA, Ambasada Ahmad Rufa’i. Adamu ya bayyana cewa dakatar da hakar ma’adanan ya biyo bayan rahoton sirri da hukumomin tsaro suka samu, inda ake zargin masu hakar ma’adanan suna matukar taimakawa wadannan ‘yan fashi da makamin da suka addabi jihar Zamfara da sauran jihohi masu makwabtaka da Zamfara din. Don haka gwamnatin Tarayya ta bada umarni kamar haka; an dakatar da hakar ma’adanai a jihar Zamfara da ma jihohin kusa da ita, sannan duk wani mai hakar ma’adanan da ya sake ya haki ma’adanai za a soke lasisin sa. Sannan wadanda ba ‘yan asalin Nijeriya bane, an basu sa’o’i 48 su tattara i-nasu-i-nasu su fice daga yankunan da ake hakar ma’adanan, sannan jami’an tsaron sun tabbatar wa da al’ummar yankunan da abun yafi shafa cewar suna iya iyawarsu don ganin sun shawo kan lamarin.

Read More at: https://hausa.leadership.ng/2019/04/07/gwamnatin-tarayya-ta-haramta-hakar-gwal-a-zamfara/

 Leadership Hausa

A daidai lokacin da kashe-kashe suka yi kamari a jihar Zamfara, gwamnatin Tarayya ta sanar da haramta duk wasu hidimomin hakar ma’adanai a fadin jihar Zamfara, sannan ta baiwa ‘yan kasashen wajen wa’adin sa’o’i 48 da su gaggauta ficewa daga yankunan da ake hakar ma’adanan.

Mukaddashin Sufeto-Janar na ‘yan sandan Nijeriya, Muhammad Adamu ne ya fitar da wannan sanarwa yau Lahadi a fadar Shugaban Kasa a yayin da ya gana sa manema labarai, a cewarshi wannan yana daga cikin kokarinsu na kawo karshen barayin Zamfara.

Babban jami’in ya bayyana hakan ne a daidai lokacin da suke tare da Shugaban Ma’aikatan fadar gwamnatin Tarayya, Abba Kyari, da darekta janar na hukumar DSS Yusuf Bichi, da kuma darekta janar na hukumar leken asiri ta Nijeriya wato NIA, Ambasada Ahmad Rufa’i.

Adamu ya bayyana cewa dakatar da hakar ma’adanan ya biyo bayan rahoton sirri da hukumomin tsaro suka samu, inda ake zargin masu hakar ma’adanan suna matukar taimakawa wadannan ‘yan fashi da makamin da suka addabi jihar Zamfara da sauran jihohi masu makwabtaka da Zamfara din.

Don haka gwamnatin Tarayya ta bada umarni kamar haka; an dakatar da hakar ma’adanai a jihar Zamfara da ma jihohin kusa da ita, sannan duk wani mai hakar ma’adanan da ya sake ya haki ma’adanai za a soke lasisin sa.

Sannan wadanda ba ‘yan asalin Nijeriya bane, an basu sa’o’i 48 su tattara i-nasu-i-nasu su fice daga yankunan da ake hakar ma’adanan, sannan jami’an tsaron sun tabbatar wa da al’ummar yankunan da abun yafi shafa cewar suna iya iyawarsu don ganin sun shawo kan lamarin.

DAGA ISYAKU.COM

Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews

 Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN