Legit Hausa
Gwamnan jihar Zamfara, Abdulaziz
Abubakar Yari, ya yi gargadin cewa nan ba da jimawa ba za a sake shiga cikin
matsananci matsi na tattalin arziki a Najeriya a sabuwar gwamnatin shugaban
kasa Muhammadu Buhari.
Kamar yadda jaridar The Nation ta
ruwaito, gwamna Yari da ya kasance shugaban kungiyar gwamnonin Najeriya ya ce
Najeriya za ta fuskanci wani sabon matsi na tattalin arziki a tsakiyar shekarar
2020.
Baya ga haka gwamna Yari yayin karin
haske dangane da yadda gwamnonin Najeriya suka yiwa kawunan su karatun ta nutsu
tare da fahimtar cewa ciyo bashi ba zai taba kubutar da kasar nan ba daga
kalubalai na tattalin arziki.
Gwamnan ya yi furucin hakan ne a
ranar Litinin yayin taron kwanaki uku na budar kai ga sabbin zababbun gwamnoni
da masu dawowa karo na biyu da aka gudanar a babban birnin kasar nan na
tarayya.
Ya ce ba bu shakka gwamnoni su daura
damara tare da kasancewa cikin shiri na bunkasa tattalin arziki a yayin
fuskantar wani sabon matsin tattalin arziki da zai auku cikin kasar nan a
tsakiyar shekarar 2020.
Gwamna Yari ya kuma bayar da
shawarar sa ta bunkasa da inganta hanyoyin karbar haraji a cikin jihohin
Najeria tare da ribatar su ta hanyoyi mafi dace na aminci domin samun madafa ta
inganta jin dadin al'umma.
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi