Legit Hausa
Hukumar yaki da cin hanci da karya
tattalin arziki (EFCC) ta bayyana dalilinta na saka damke korarriyar alkaliyar
babbar kotun tarayya, Jastis Rita Ofili-Ajumogobia. A wani jawabi da shugaban
sashen yada labarai da sadar wa, Tony Orilade, ya fitar a yau, Talata, EFCC ta
ce ta sake kama Ofili-Ajumogobia ne domin samun damar sake shirya wasu sabbin
tuhume-tuhume a kan ta. Sanarwar ta kara da cewa, kama Ofili-Ajugomobia, ya
biyo bayan wani hukunci da kotun daukaka kara a Legas karkashin Jastis
Hyeladzira Nganjiwa ta taba yanke wa a kan cewar, ba za a iya gurfanar da
alkali ko alkaliya ba har sai an kore shi daga aiki ko kuma hukumar kula da
bangaren shari'a (NJC) tayi masa ritayar dole.
EFCC ta ce ta gurfanar da Jastis
Ofili-Ajumogobia a gaban NJC kuma tunda sun dauki mataki a kan ta, yanzu zasu
tunkari kotu da sabbin tuhume-tuhume a kan ta. An fara gurfanar da
Ofili-Ajumogobia da babban lauyan Najeriya (SAN), Godwin Obla, a ranar 30 ga
watan Nuwamba na shekarar 2016 a kan wasu tuhume-tuhume 30 da suka hada da cin
hanci, bayar da da bayan karya, tauye hukunci da sauransu. Daga baya hukumar
EFCC ta gyara tuhumar da ta ke yi masu daga guda 30 zuwa 31.
Kafin fitar da jawabin na EFCC,
Legit.ng ta sanar da ku cewar ana ta tafka takaddama a harabar babbar kotun
Ikeja, yayin da jami'an hukumar yaki da cin hanci da rashawa (EFCC) suka mamaye
kotun domin cafke tsohuwar mai shari'ar a babbar kotun gwamnatin tarayya, Rita
Ofili Ajumogobia. Wannan kuwa ya biyo bayan watsi da karar da aka shigar ta
laifuka 30 da EFCC ke tuhumar mai shari'a Ajumogibia da aikatawa, gaban mai
shari'a Hakeem Oshodi. Ajumogibia na fuskantar tuhuma kan laifukan da suka
shafi cin hanci da rashawa da kuma amfani da ofishinta ta hanyar da ba ta dace
ba.
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi