Amfani da mafarauta zai kawo karshen garkuwa da mutane a Nigeria - Sarki Sanusi


Legit Hausa

Sarkin Kano, Muhammad Sanusi II ya shawarci gwamnatin tarayya da ta yi amfani da mafarauta domin magance matsalar garkuwa da mutane da sauran ayyukan ta'addanci da ke ci gaba da mamaye shiyyar Arewacin Nigeria.

Sarki Sanusi, wanda ya bada wannan shawarar a yayin wani taro na shuwagabannin mafarauta a Kano a ranar Lahadi karkashin kungiyar masu kishin ci gaban jihar Kano (KCCI), ya ce jihar Kano ta gwada irin hakan, kuma an samu nasara.

Da ya samu wakilcin hakimin Doguwa, Dan Amar na Kano, Alhaji Aliyu Harazimi, Sanusi ya ce a cikin shekaru hudun da suka gabata, Kano ta Kudu ta kasance cikin fargaba saboda yawaitar garkuwa da mutane da kuma fashi da makami. Ya ce:

"A lokacin da garkuwa da mutane ya tsananta a dajin Falgore da ke karamar hukumar Doguwa, mun gayyaci mafarauta kuma muka samar da watatawagar tsaro ta musamman da suka hada da sojoji, 'yan sanda, civil defence da maharba.

"Mun samu nasarar lalata sansanonin masu garkuwa da mutane guda shida da ke a cikin dajin. A yanzu dai shekaru hudu ke nan tunda jami'an suka kai wannan sumame, har yanzu bamu sake jin an yi garkuwa da wani a dajin ba." Sarki Sanusi ya baiwa gwamnatin tarayya shawara kan cewar ya kamata ta samar da makamanciyar wannan tawagar domin kawo karshen garkuwa da mutane a jihohin Zamfara Kaduna da sauran jihohin da lamarin ya shafa.


DAGA ISYAKU.COM

Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews

 Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN