Legit Hausa
Abiola Ajimobi, gwamnan jihr Oyo, ba zai cigaba da halartar yakin neman zaben dan takarar gwamnan a karkashin inuwar jam’iyyar APC a jihar sa ba, kamar yadda majiyar mu ta bayyana ma na.
Ajimobi ya sha kaye a hannun
jam’iyyar PDP a zaben kujerar sanatan jihar Oyo ta kudu da ya yi. Gwamnan ya
samu kuri’u 92,579 yayin da dan takarar jam’iyyar PDP, Dakta Kola Balogun, ya
samu kuri’u 105,720. Wani lamari da ya kara bayar da mamaki shine yadda
jam’iyyar PDP ta lashe zaben kujeru 4 daga cikin 5 na ‘yan majalisar wakilai da
yankin na jihar Oyo ta kudu ke da su.
Faruwar hakan ne ta saka jagoran
jam’iyyar APC na kasa, Bola Tinubu, ya karbi ragamar yakin neman zaben dan
takarar gwamnan jihar ta Oyo a jam’iyyar APC domin ganin PDP ba ta kwace jihar
ba.
Majiyar mu ta sanar da mu cewar
yanzun haka Tinubu ya saye takarar tsohon gwamnan jihar, Alao Akala, domin kara
wad an takarar APC, Bayo Adelabu, karfi sannan ya umarci gwamna Ajiomobi ya
nesanta kan sa daga wurin yakin neman dan takarar.
Wata majiyar jam’iyyar APC ta shaida
wa majiyar mu cewar, “Tinubu ya fahimci cewar jama’ar jihar Oyo na jin haushin
gwamna Ajimobi ne ba jam’iyyar APC ba. “Abin tsoron shine zuwan Ajimobi wurin
kamfen din Adelabu zai kara lalata damar da APC ke da shin a yin nasara a zaben
gwamnoni da za a yi karshen mako.”
DAGA ISYAKU.COM
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi