Legit Hausa
Shugabanin jam'iyyar All
Progressives Congress (APC) na yankin Kudu maso Kudancin Najeriya sun nemi a
basu mukammin shugaban majalisar dattawa na kasa.
Sun mika wannan bukatan ne cikin
sakon taya murna da suka aike wa Shugaba Muhammadu Buhari a kan nasarar da ya
samu na lashe zaben shugban kasa na ranar 23 ga watan Fabrairun 2019.
A sakon da suka fitar a ranar
Laraba, mataimakin shugaban jam'iyyar APC na Kudu maso Kudu, Ntufam Etta ya ce
yankin ta cancanci a bata wannan matsayin. Ya ce, "Yankin mu ta dade tana
bayar da gudun mawa domin ganin kasar mu ta cigaba kuma za mu cigaba da yin
hakan.
"Shugabanin jam'iyyar mu sun taka
muhimmiyar rawa wurin tabbatar da zaman lafiya a yankin domin ganin kasuwancin
ta cigaba da kuma wayar da kan matasan mu kan muhimmancin zaman lafiya.
"Muna mika godiyar mu ga dukkan shugbanin yankin da matasa bisa goyon
bayan da suka bawa shugbaban kasa domin ya cigaba a ayyukan cigaba.
Zamanin da matasan mu ke tayar da
kayan baya domin hana cigaba ya wuce." Ya kara da cewa, "Mun tuna cewa
dan mu Sanata Joseph Wayas ya rike mukamin shugaban majalisar dattawa kuma ya
taka rawar gani.
A karkashin shugabancin sa, fadar
shugaban kasa da majalisa da sashin shari'a sunyi aiki cikin lumana domin
cigaba 'yan Najeriya. "Saboda haka, zaben shugaban majalisa daga Kudu maso
Kudu zai daidaita siyasar kasar nan domin majalisa ta mayar da hankali a kan
tsara dokoki.
Kazalika, zaben shugaban majalisa daga yankin
mu zai hana afkuwar matsala a cikin fadar shugaban kasa kamar yadda muka gani a
baya."
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi