Legit Hausa
Mambobin jam’iyyar APC a majalisar dattijai sun shaidawa
majiyar mu cewar sabon shugabancin majalisar da za su kafa a watan Yuni zai
binciki shugabancin majalisar da Sanata Abubakar Bukola Saraki ya shafe shekaru
hudu ya na yi.
Sanatocin na jam’iyyar APC da su ka yi nasara sake lashe
zaben da aka yi satin da ya gabata sun bayyana cewar shugabancin majalisar zai
binciki yadda Saraki ya yi amfani da kudaden da majalisar ke da su a tsawon
shekaru hudu da ya yi ya na jagoranci. Saraki ya zama shugaban majalisar
dattijai ne a shekarar 2015 a cikin wani yanayi mai tsanani da rudani saboda
takun saka da ke tsakanin sa da fadar shugaban kasa da shugabancin jam’iyyar
APC.
Daga bisani Saraki ya fice daga jam’iyyar APC ya koma
tsohuwar jam’iyyar sa, PDP, da ya mulki jihar Kwara na tsawon shekaru 8 a cikin
ta. Sai dai, Saraki, ya sha kaye a zaben shugaban kasa da na mambobin majalisar
tarayya da aka gudanar a makon jiya, lamarin da ya kawo karshen zaman sa a
majalisar dattijai.
Wani daga fitattun sanatocin APC ya sanar da majiyar mu
cewar, “akwai yiwuwar mu binciki Saraki. Mun san cewae zai kokarin ganin ya
kafa magajin sa wanda ba zai bincike shi ba. Akwai yiwuwar zai goyi bayan wanda
ya san ya na da kusanci da shi domin ya zama sabon shugaban majalisar “Amma
maganar gaskiya shine akwai dalilai da hujjoji na binciken Saraki kuma za mu
tabbatar mun matsa lamba an bincike shi, musamman a kan laifuka da su ka shafi
yadda ya yi amfani da kasafin kudin majalisa a cikin shekaru hudu da su ka
gabata,” a cewar wani Sanata da ya bukaci a boye sunan sa.
Kazalika wani Sanatan da bai yarda a ambaci sunan sa bay a
kara da cewa, “har yanzu Saraki bai hakura ba don kuwa ya na nan ya na kokarin
ya kafa wanda zai zama sabon shugaban majalisar dattijai. Burin sa shine
jam’iyyar PDP ta cigaba da shugabancin majalisar dattijai.
“Ya na tuntubar sanatocin APC da na PDP domin ganin ya kafa
na kusa da shi ya zama shugaban majalisar dattijai, sai dai za mu tabbatar da
cewar duk wani mai kusanci da Saraki bai samu wata kujerar shugabanci daga
cikin kujerun shugabannin majalisar dattijai ba.” Da aka tuntubi Yusuph
Olaniyonu, mai taimaka wa Saraki a bangaren yada labarai, ya ki cewa komai a
kan wannan batu.
DAGA ISYAKU.COM
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi