Legit Hausa
Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ce mutane ma su kima da
kishin Najeriay ne kawai za su mukamai a nade-naden da zai yi a sabuwar
gwamnatin sa.
Kazalika ya yi alkawarin kara yawan mata da matasa a cikin
sabbin nade-naden saboda irin muhimmiyar gudunmawar da su ka bayar wajen samun
nasarar sa a zaben da aka yi a karshen makon jiya. Ya bayyana cewar gwamnatin
sa ba zata bawa mata da matasa kunya ba.
Buhari ya yi wadannan kalamai ne yayin gabatar da jawabi a
wurin liyafar da mata da matasan jam’iyyar APC su ka shirya ma sa omin taya shi
murnar samun nasarar lashe zaben kujerar shugaban kasa a karo na biyu. Ya ce
samar da taki a kan farashi mai rahusa ya kawo habakar samun amfanin gona da
kuma rage yawan shigowa da kayan abinci daga kasashen ketare.
Buhari ya yi kira ga matasan Najeriya da su rungumi noma
domin kawar da yunwa da samun hanyoyin dogaro da kai. Kazalika, ya soki shekaru
16 na mulkin PDP tare da zargin su da barnatar da dumbin dukiyar kasa da
Najeriya ta samu a lokacin.
DAGA ISYAKU.COM
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi