Legit Hausa
Jam'iyyar Peoples Democratic Party, PDP, ba ta amince da
sakamakon zaben shugaban kasa da na 'yan majalisu da hukumar zabe mai zaman
kanta INEC ke fitarwa ba a halin yanzu.Shugaban PDP na kasa, Prince Uche
Secondus wanda a halin yanzu ya kira taron manema labarai a babban birnin
tarayya Abuja ya ce kuri'un da INEC ke sanarwa ba dai-dai bane kuma ba za su
amince da hakan ba.
A wata labarin, Sanata Shehu Sani mai wakiltar Kaduna ta
Tsakiya na jam'iyyar PRP ya nemi hukumar INEC ta soke zaben 'yan majalisun
tarayya da aka gudanar a jihar Kaduna.
Shehu Sani ya yi ikirarin cewa an tafka magudi a garuruwa da
yawa da ke karkashin mazabarsa kuma ya ce idan har INEC na son yin adalci ya
zama dole ta soke zaben. Ku biyo mu domin samun karin bayani
DAGA ISYAKU.COM
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi