Canja Sheka Zuwa APC: Gwamna Tambuwal Ya Sallami Kwamishinan Watsa Labarai na Jihar Sokoto

Gwamnan jihar Sokoto Aminu Tambuwal ya sallami Kwamishinan watsa labarai na jihar Mr Bello Muhammad-Goronyo daga mukaminsa da yammacin Talata, sakamakon ficewar Kwamishinan daga jam'iyar PDP zuwa jam'iyar APC .

Darakta janar kan sadarwa da hulda da jama'a na Gwamna Aminu Tambuwal  Mallam Abubakar Shekara, ya shaida wa manema labarai haka, ya ce " Gwamna Aminu Tambuwal ya sallami Barista Bello Goronyo daga mukamin Kwamishinan watsa labarai na jihar Sokoto nan take. Kuma ya umarci Sakataren dindindim na ma'aikatan watsa labarai na jihar Sokoto ya rike ma'aikatar".

Ya kara da cewa an sallami Kwamishinan ne bisa zargin yin zagon kasa ga ayyukan alhairi da Gwamnati ta yi.

Shi dai tsohon Kwamishinan ya ayyana ficewarsa ne daga jam'iyar PDP a wani gangamin taro na jam'iyar APC a Goronyo da yammacin Talata.

DAGA ISYAKU.COM

Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/KIHbQShlAs2GexpIYyxleG

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN