Type Here to Get Search Results !

Canja Sheka Zuwa APC: Gwamna Tambuwal Ya Sallami Kwamishinan Watsa Labarai na Jihar Sokoto

Gwamnan jihar Sokoto Aminu Tambuwal ya sallami Kwamishinan watsa labarai na jihar Mr Bello Muhammad-Goronyo daga mukaminsa da yammacin Talata, sakamakon ficewar Kwamishinan daga jam'iyar PDP zuwa jam'iyar APC .

Darakta janar kan sadarwa da hulda da jama'a na Gwamna Aminu Tambuwal  Mallam Abubakar Shekara, ya shaida wa manema labarai haka, ya ce " Gwamna Aminu Tambuwal ya sallami Barista Bello Goronyo daga mukamin Kwamishinan watsa labarai na jihar Sokoto nan take. Kuma ya umarci Sakataren dindindim na ma'aikatan watsa labarai na jihar Sokoto ya rike ma'aikatar".

Ya kara da cewa an sallami Kwamishinan ne bisa zargin yin zagon kasa ga ayyukan alhairi da Gwamnati ta yi.

Shi dai tsohon Kwamishinan ya ayyana ficewarsa ne daga jam'iyar PDP a wani gangamin taro na jam'iyar APC a Goronyo da yammacin Talata.

DAGA ISYAKU.COM

Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/KIHbQShlAs2GexpIYyxleG

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi

Top Post Ad

Below Post Ad

Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN