Legit Hausa
Babban malamin addinin musulunci
kuma jigo a kungiyar Jama’atul Izalatul Bidi’a Waikamatus Sunnah, (JIBWIS)
Sheikh Yusuf Sambo Rigachikun ya ce dan takarar shugabancin kasa na PDP Atiku
Abubakar zai jefawa kuri'a a zaben 2019.
A kwana kwanan nan ne shugabanin
kungiyar Izala na kasa suka bukaci 'ya'yan jam'iyyar su zabi dan takarar
jam'iyyar APC, Shugaba Muhammadu Buhari a yunkurinsa na neman zarcewa karo na
biyu. A hirar da ya yi da wakilin BBC, Mustapha Kaita, Sheikh fadi dalilin da
yasa zai zabi Atiku Abubakar. "Zan zabi dan takarar da yafi taimakon
addinin Musulunci da taimakon al'ummar kasa da amfanar da sum," a cewar
Sheikh Sambo.
Babban malamin ya yi ikirarin cewa
ya kwashe shekara 30 da sanin Atiku kuma ya ce Atikun ya gina masallatan Juma'a
fiye da 100. Wannan ra'ayin nasa ya sha banban da na shugaban kungiyar na kasa,
Sheikh Abdullahi Bala Lau da ya ce kungiyar ta cimma matsayar zaben Buhari ne
bayan wani taro da suka gudanar.
Shugaban masu da'awah na kungiyar,
Ibrahim Jalo-Jalingo ya ce kungiyar ta cimma matsayan goyon bayan Buhari ne
saboda nasarorin da gwamnatinsa ta samu a fanin yaki da rashawa, yaki da 'yan
ta'addan Boko Haram, farfado da noma da tattalin arzikin Najeriya.
"Al'umma sunyi na'am da
nasarorin da gwamnatin Buhari ta samu cikin shekaru uku da rabi hakan yasa muka
yanke shawarar fadawa mambobin mu su zabi Shugaba Muhammadu Buhari da sauran
'yan takarar da ke aiki tare da shi," inji shi. A cewar babban malamin,
gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari tana kan alkibla shi yasa kungiyar Izala ke
goyon bayan ta.
DAGA ISYAKU.COM
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/KIHbQShlAs2GexpIYyxleG
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi