Shugaba Buhari Ya Nada Shugabannin Farfadowa Da Yankin Arewa Maso Gabas

Hausa Legit


Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya nada shugabannin hukumar kula da ci gaban yankin arewa maso gabashin kasa da rikicin Boko Haram ya daidaita. Shugaban majalisar dattawa, Bukola Saraki nae ya bayyana haka yayin karanta wasikar da shugaban kasar ya rubuta wa Majalisar domin tantance sunayen.

Sunayen wadanda Buhari ya gabatar sune Manjo Janar Paul Terfa a matsayin shugaba, sai kuma Mohammed Goni Alkali a matsayin Babban Daraktan Gudanarwa tare da Musa Uma Yashi a matsayin Daraktar Jinkai da Mohammed Jawa a matsayin Daraktan kudi da mulki.

Sauran sun hada hada da Umar Maiwada Mohammed a matsayin Daraktan Ayyuka da kuma wakilan shiyoyi 6 na yankunan kasar, wato David Sabo Kante daga Arewa Maso Gabas da Asamo Mohammed daga Arewa Maso Yamma da Benjamin Adeniyi daga Arewa ta Tsakiya da Olawale Osun daga Kudu Maso Yamma, sai Theo Nkechi daga Kudu Maso Gabas da Bassey Uke daga Kudu Maso Kudu.

Yankin Arewa Maso Gabashin Najeriya ya tagayyara sakamon dogon lokacin da mayakan Boko Haram suka dauka na kaddamar da hare-hare, abin da ya haddasa asarar rayukan dimbin jama'a tare da gurgunta tattalin arzikin yankin, baya ga tilasta wa miliyoyin mutane kaurace wa gidajensu.


DAGA ISYAKU.COM

Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/KIHbQShlAs2GexpIYyxleG

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN