Gwamnatin Trayya Ta Amince Da Biyan N30.000 Karin Albashi Ga Ma'aikata


Legit Hausa

Bayan taron majalisar zartarwa (FEC) da shugaba Buhari ya jagoranta a jiya, Talata, gwamnatin tarayya ta sanar da niyyarta na mika shawarar da ta yanke a kan karin albashi ga kwamitin masu ruwa da tsaki a harkar tattalin arziki(NEC).

Jaridar Punch ta rawaito cewar a wurin taron FEC na jiya, gwamnatin tarayya ta amince zata biya N30,000 a matsayin mafi karancin albashi kuma zata sanar da NEC a ganawar da zasu yi gobe, Alhamis, 17 ga watan Janairu.

NEC ta kunshi gwamnonin jihohin Najeriya, gwamnan babban bankin kasa (CBN), wasu manyan ministoci, da ma'aikatu da hukumomin gwamnati. Da yake magana da manema labarai a kan batun, ministan yada yada labarai da al'adu, Lai Mohammed, ya ce za a tattauna batutuwa da dama da FEC ta amince dasu.

A cewar sa, "ba zan iya baku cikakkun bayanai a kan abubuwan da muka tattauna ba tunda zamu tattauna a kansu a ganawar mu da NEC ta ranar Alhamis. Zamu sanar da shawarwarin da muka yanke bayan ganawar."Ko a ranar 13 ga watan Disamba na shekarar 2018, sai da gwamnonin Najeriya suka yi wani taro a Abuja domin cigaba da tattaunawa a kan batun na karin albashi.
 

DAGA ISYAKU.COM

Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/KIHbQShlAs2GexpIYyxleG

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN