Type Here to Get Search Results !

Main event

'Yar shekara 9 ta maka Gwamnatin Ogun a Kotu tana neman a biyata N1m | isyaku.com

Wata yarinya 'yar shekara tara Aisha AbdulAleem, ta maka Gwamnatin jihar Ogun tare da shugaban karamar Makarantar Sakandarae ta Gateway Mrs Kushimo a gaban wata babban Kotu jiha da ke Isalo a Abeokuta, bisa zargin cin zarafinta ta hanyar hanata saka Hijabi a Makarantar

Aisha ta hannun Mahaifinta Mr. Muhammad AbdulAleem, ta gurfanar da shugabar Makarantar ne a Kotu saboda ta cire wa Aisha Hijabi da karfin tsiya, kuma ta hanata shiga aji domin ta dauki darasin karatu..

Cikin wadanda ake kara har da Kwamishinan Ilimi na jihar Ogun, Atoni janar kuma Kwamishinan shari'a na jihar Ogun, da kuma Gwamnatin jihar Ogun.

Lauyan Aisha, Olusoji Odutan, ya ce an shigar da karar ne domin neman Kotu ta haramta mataki da Makarantar ta dauka na hana Aisha shiga Makarantar da Hijabi. Ya ce yana kuma bukatar Kotu ta ayyana cewa wannan mataki haramtacce ne.

DAGA ISYAKU.COM

Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/KIHbQShlAs2GexpIYyxleG

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi

Top Post Ad

Below Post Ad

Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN

Hollywood Movies