Wani Farfesa ya yi kacakaca da kasar Israila kan kin janyewa daga Falasdinu

TRT Hausa
Jaridun Isra'ila sun yi caa kan Farfesa George P. Smith na jami'ar Missouri da ke Amurka,sakamakon yadda ya caccaki gwamnatin kasarsu game da zalunci da kuma gallaza wa Falasdinu da ta ke yi babu gaira babu dalili.

Smith,wanda ya karbi goron gayyatar da Hadakan Kwararrun Masana Masu Kishin Falasdinu suka aika masa,bayan ya halarci bikin karbar lambar yabo ta zaman lafiya ta Nobel da aka shirya a Stockholm, babban birnin kasar Swizerland,da zummar tattaunawa kan lamirin Falasdinu da ya ki ya ki cinyewa.

A yayin wannan muhimmin taron, farfesan ya ce: "Isra'ila na ci gaba da yin wancakali da dokokin kasa da kasa da kuma yin kunnen uwar shegu kan batun janyewa ko dakatar da mamayar Falasdinu".

Masanin ya ci gaba da cewa, "Ayyana Isra'ila da Falasdinu a matsayin kasashe biyu masu cin gashin kansu ita ce hanya mafi sauki da kuma a'ala wajen kawo warware  bakin zaren wannan rikicin da ya ki ci ya ki cinyewa.A lokacin ne za a samu dauwamammen zaman lafiya.

Haka zalika kasashen biya zasu ci gaba da zama bakwabtan juna salim-alim ba tare wata matsa ta sake kunno kai ba.Amma alamu na nuna mana cewa halayen Isra'ilayawa sun sha bamban da dukannin wadannan manufofin.Sun ki yarda a cimma masalaha, saboda basa bin sharuddan  aka gindaya musu.

Idan har ana son a zauna lafiya, to dole ta maida wa Falasdinu yankunta da ta mamaye da kuma biya hakkokin Falasdinawa da taka.Ba zamu taba da yarda ababen da Isra'ila ke ci gaba da yi a Zirin Gaza.Babu wani abu da Isra'ila ke yi a yankin face gallaza wa Falasdinawa.Har ma da Yahudawa da suka ki goya ma ta baya kan  zaluncin da ta ke ci gaba da yi Falasdinawa ma, ba su tsira daga kaidinta ba.Ya ci a ce Isra'ila ta dakatar da wannan ta'asar".

A bana,Farfesa Frances H. Arnold da takwarorinsa, George P. Smith  da Gregory P. Winter  ne suka lashi lambar yabo ta Nobel a fannin ilimin sinadirai,sakamakon muhimmiyar gundumowar da suka kawo a fannin cigaban akidar juyin juya hali.

Isra'ila ta matukar bakin cikin ganin Farfesa Smith ya lashe lambart yabo ta Nobe.Tuni dai jaridun kasar Yahudu suka tayar da jijiyoyin wuya kan wannan nasarar da shahararren masanin ya yi, ganin yadda ya dinka sukar lamirin gwamnati da kuma manufofin kasarsu.

DAGA ISYAKU.COM

Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/KIHbQShlAs2GexpIYyxleG

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN