Legit Hausa
Jaridar Thisday tayi wata hira mai tsayi da malamin addinin Islama, Sheikh Ahmad Gumi, a kan harkokin da suka shafi kasa da kuma batutuwa masu alaka da zaben shekarar 2019. Da yake amsa tambaya a kan irin shawarar da zai bawa 'yan siyasar Najeriya, Shehun Malamin ya shawarci 'yan takara su saka bukatar kasa a gaba a cikin manufofinsu na yakin zabe.
Jaridar Thisday tayi wata hira mai tsayi da malamin addinin Islama, Sheikh Ahmad Gumi, a kan harkokin da suka shafi kasa da kuma batutuwa masu alaka da zaben shekarar 2019. Da yake amsa tambaya a kan irin shawarar da zai bawa 'yan siyasar Najeriya, Shehun Malamin ya shawarci 'yan takara su saka bukatar kasa a gaba a cikin manufofinsu na yakin zabe.
Da aka tambayi Sheikh Gumi ko mai zai ce a kan shawarar da
shugaba Buhari ya bawa malaman addini a kan su nesanta kansu daga harkokin
siyasa domin kare mutuncinsu, sai ya kada baki ya ce, "a'a, abinda yake
son fadi a fakaice shine malaman addinin Islama da Kirista su daina sukar sa.
Idan ba zamu yaudari kan mu ba, mun san cewar malaman addini mutane ne kamar kowa kuma suna da bukatu kamar yadda ragowar jama'a keda su; suna son ganin an samu shugabanni nagari da zasu taimaki al'umma bakidaya. Na san tabbas akwai malaman dake fakewa da addini domin biyan bukatar kansu, amma akwai wadanda kishin kasa ne a gabansu.
Idan ba zamu yaudari kan mu ba, mun san cewar malaman addini mutane ne kamar kowa kuma suna da bukatu kamar yadda ragowar jama'a keda su; suna son ganin an samu shugabanni nagari da zasu taimaki al'umma bakidaya. Na san tabbas akwai malaman dake fakewa da addini domin biyan bukatar kansu, amma akwai wadanda kishin kasa ne a gabansu.
Gumi ya musanta cewar yana sukar gwamnatin shugaba Buhari da
yawa, tare da bayyana cewar ya dade yana sukar gwamnatoci a baya kuma ba zai
daina ba sai an samu gyara a yadda ake tafiyar da gwamnati a kasar nan.Sai dai,
ya ce gwamnatin Buhari na yaudarar jama'a ne kawai da batun yaki da cin hanci
bayan a zahiri sun mayar da yin arziki a lokacin mulkinsu laifi.
Kazalika ya soki gwamnati a kan cigaba da tsare shugaban
mabiya mazahabar Shi'a, Sheikh Ibrahim El-Zakzaky, da kuma artabu da nagoya
bayansa dake zanga-zangar neman sakinsa, yana mai bayyan cewar mabiya Shi'a
'yan kasa ne kamar kowa dake da hakkin yin addininsu kamar kowa.
DAGA ISYAKU.COM
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/KIHbQShlAs2GexpIYyxleG
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi