Type Here to Get Search Results !

Dalili Da Ya Sa Aka Yi Ma Buhari Ihu A Zauren Majalisa - 'Yar Majalisar Wakilai Ta PDP | isyaku.com

Wata 'yar Majalisar wakilai kuma mai magana da yawun masu tafiyar da kwamitin yakin neman zabe na shuagan kasa a jam'iyar PDP Nnena Ukeje ta ce dalilin da ya sa 'yan Majalisa suka yi ma shugaba Buhari ihu a zauren Majalisa yayin da ya gabatar wa Majalisa da kasafin kudi na 2019 shi ne " Marmakin Buhari ya fuskanci abin da ya kawo shi zauren Majalisa, sai ya mayar da lamarin tamkar yakin neman zabe na jam'iyar APC a matsayinshi na wanda ke rike da tutar 'dan takarar jam'iyar APC".

Ta yi wannan jawabi ne yayin da ta bayyana a gidan Talabijin na Channels ranar Litinin. Ta kara da cewa " abin da shugaba Buhari ya kamata ya yi shi ne, "Da ya koyi halin tsohon shugaba Jonathan, wanda ya gabatar da kasafin kudi kafin zaben a yanayi na saukin kai da fahimta".

" A wannan yanayi da lamura suka yi zafi, shugaba Buhari har ma ya daga hannayensa guda biyu daidai yadda APC ke nuna zarcewa a yanayin yakin neman zabensu. Irin wannan hali dole ne ya zafafa lamurra a wannan lokaci domin dai akwai 'yan jam'iyar PDP masu yawa a wannan zaure da 'yan jam'iyar APC suka dau shewa daidai lokacin da shugaba Buhari ya yi wadannan ababen".

"A matsayinka na 'dan Najeriya, kamata yaa yi ka auna ka gani, shin rayuwarka ta inganta tun 2015 zuwa yanzu ko a'a ? wannan shi ne ya kama kowane 'dan Najeriya ya duba".

DAGA ISYAKU.COM

Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/KIHbQShlAs2GexpIYyxleG

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi

Top Post Ad

Below Post Ad

Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN