'Yan kasuwar shanu 15 daga jihar Kebbi sun mutu a hanyar su ta kai dabbobi Lagos


Legit Hausa

Kamfanin dillancin labarai na kasa (NAN) ya rawaito cewar 'yan kasuwar daga garuruwan Andare, Katenga, da Maiyama, na hanyar su ta zuwa cin kasuwar shanu a jihar Legas lokacin da hatsarin ya ritsa da su. Rahoton NAN ya bayyana cewar motar da ke dauke da 'yan kasuwar da shanunsu ta kwacewa direba a kan hanyar Maiyama zuwa Koko, sannan ta wuntsila zuwa cikin daji.

Wani shaidar gani da ido, Garba Maiyama, ya shaidawa NAN cewar, "mutane 15 daga cikin 'yan kasuwar dabbobin take su ka mutu kuma tuni aka mika su ga iyalansu domin yi masu jana'iza kamar yadda Musulunci ya tanada. "Babban abin tashin hankalin shine yadda a gida daya mutane 5 su ka mutu a hatsarin.

"Bamu san abinda ya haddasa hatsarin ba gaskiya," a kalaman shaidar. Sai dai kakakin rundunar 'yan sanda a jihar Kebbi, DSP Danjuma Possy, ya shaidawa NAN cewar ya zuwa yanzu dai ba a sanar da su batun hatsarin ba.
 

DAGA ISYAKU.COM

Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/KIHbQShlAs2GexpIYyxleG

Domin Gyara Wayarka Ka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN