Type Here to Get Search Results !

'Yan kasuwar shanu 15 daga jihar Kebbi sun mutu a hanyar su ta kai dabbobi Lagos


Legit Hausa

Kamfanin dillancin labarai na kasa (NAN) ya rawaito cewar 'yan kasuwar daga garuruwan Andare, Katenga, da Maiyama, na hanyar su ta zuwa cin kasuwar shanu a jihar Legas lokacin da hatsarin ya ritsa da su. Rahoton NAN ya bayyana cewar motar da ke dauke da 'yan kasuwar da shanunsu ta kwacewa direba a kan hanyar Maiyama zuwa Koko, sannan ta wuntsila zuwa cikin daji.

Wani shaidar gani da ido, Garba Maiyama, ya shaidawa NAN cewar, "mutane 15 daga cikin 'yan kasuwar dabbobin take su ka mutu kuma tuni aka mika su ga iyalansu domin yi masu jana'iza kamar yadda Musulunci ya tanada. "Babban abin tashin hankalin shine yadda a gida daya mutane 5 su ka mutu a hatsarin.

"Bamu san abinda ya haddasa hatsarin ba gaskiya," a kalaman shaidar. Sai dai kakakin rundunar 'yan sanda a jihar Kebbi, DSP Danjuma Possy, ya shaidawa NAN cewar ya zuwa yanzu dai ba a sanar da su batun hatsarin ba.
 

DAGA ISYAKU.COM

Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/KIHbQShlAs2GexpIYyxleG

Domin Gyara Wayarka Ka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi

Post a Comment

0 Comments
* Please Don't Spam Here. All the Comments are Reviewed by Admin.
Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN