Shari'ar Maryam Sanda: Shedu sun fadawa kotu yadda aka kashe Bilyaminu


 Legit hausa

A yau Alhamis ne shedu uku suka bayyana wa kotu yadda aka yi Bilyaminu Bello da ake zargin matarsa, Maryam Sanda da kashe shi ya mutu. Bello, dan tsohon shugaban jam'iyyar PDP na kasa, Haliru Bello ya rasu ne a Nuwamban 2017.

An tuhumar matarsa Maryam Sanda, mahaifiyarta, Maimuna Aliyu; dan uwanta, Aliyu Sanda da mai aikin gidansu, Sadiya Aminu da hannu cikin kisarsa. A yau Alhamisa ne lauya mai shigar da kara, Fedelis Ogbebe ya gabatarwa kotu shedu uku, Hamza Abdullahi (mai wanki da guga), Simon Okon da Usman Aliyu domin su bayyana kotu abinda suka sani a kan rasuwar Bilyaminu. Ga abinda Mr Abdullahi mai wanki da guga a gidan ya fadi:

"A ranar 17 ga watan Nuwamban 2017 misalin karfe 1-2 na dare ina kwance sai na ji ihun Bilyaminu, na tashi na nufi idan ya ke sai na samu ya rufe bangaren kirjinsa da riga, bayan mintuna biyu sai matarsa ta fito rike da makulin mota ta bukaci mu taimake ta saka Bilyaminu cikin mota.

 "Da mu kayi kokarin daga shi sai muka ka jini. Ni da wasu mutane biyu muka saka shi cikin mota yayin da matarsa ta tuka motar. Da muke cikin motar ta tambayi ni Asibiti mafi kusa sai na fada mata Maitama Clinic. "Da isar mu asibitin mun hada da nurse ta da kira mana likita. Likitan ya tambayi Maryam abinda ya faru har sau uku amma ba ta amsa ba.

Hakan yasa likitan ya ce mu tafi dashi wani asibiti, daga nan muka tafi Maitama General Hospital nan ma likita ya tambaya abinda ya faru. "Daga nan ne Maryam ta fada wa likitan cewa suna ta fada ne da mijinta tunda safe. Likitan ya duba Bilyaminu sai ya gano cewar ya mutu. Likitan ya bukaci ta kira 'yan uwansu a waya amma ta ce masa wayanta da na mijinta sun lalace wajen fada.

Ya bata wayansa ta kira yan uwanta ta fada musu abinda ya faru. "Yan uwanta sun taho daga baya suka karbi gyalenta suka rufe gawar Bilyaminu. Daga nan mahaifiyar Bilyaminu ta iso ta bude fuskan dan ta inda ta lura akwai alamar yankan wuka a kirjinsa da cizo a kirjinsa da kunnensa. Akwai yanka a yatsansa da kuma al'auransa.

 "Da komawarmu gida sai na lura cewa an goge jinin da muka bari kafin zuwa asibiti, na tambayi Alabi ko shine ya goge jinin amma ya ce ba shi bane." Mr Okon ASP na yan sanda shima ya bayar da nasa labarin abinda ya sani. Kazalika Mr Aliyu, abokin Bilyaminu shima ya fadawa kotu abinda ya sani game da rasuwar. Bayan sauraron dukkan shaidun, alkalin kotun mai shari'ah Yusuf Halilu ya dage cigaba da sauraron shari'ar zuwa ranar 26 ga watan Nuwamba.
 

DAGA ISYAKU.COM

Copyright, do not copy and paste our news on your blog without express written permission from us.

Shiga shafin mu na Facebook facebook.com/isyakuweb

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/AlFUDQouyehJRacXxBzbX0

Domin Flashin ko gyaran wayarka Garzaya zuwa SENIORA TECH,shago mai lamba 50, hawa na sama gefen hagu,TAUSHI PLAZA , yamma daga gidan marigayi Waziri Umaru,kan Tiltin Ahmadu Bello, Nassarawa, Birnin kebbi jihar Kebbi. Barka da zuwa gidan sauki wajen gyaran wayar salula a garin Birnin kebbi.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN