Kebbi: Zamu kowo karshen muggan ayyuka a kasar Zuru - Shugabannin Fulani

Daga Abba M. Zuru

An yi kira ga al’ummar Fulani na kasar Zuru da su kasance masu bin doka da oda, shugaban Fulani na kasar Zuru kuma shugaban kungiyar Miyetti Allah na kasa Alhaji Kirwa, ya yi wannan kira a cikin jawabinsa a wajen taron na al’umman Fulani na kasar Zuru da aka gudanar a babban dakin taro na Komo Unity Hall a garin Zuru.

Alhaji Kirwa ya kara da cewa gwamnatin tarayya karkashin jagorancin shugaba Muhammadu Buhari da ta jihar Kebbi karkashin gwamna Abubakar Atiku Bagudu, suna matukar kokarin ganin sun inganta rayuwar Fulani ta hanyar mayar masu da mashekarinsu,burtallai da gina masu Dam tare da basu abincin dabbobi.Sakamokon haka godiyansu ga wannan gwamnati shine tsare doka.

Ardon Zuru ya yi kira ga al’ummar Fulani su guji shaye shaye wanda shi ne ummul haba’is na samun masu aikata mugan laifuka a cikinsu kamar fashi da makami da kuma satar mutane.

A nashi jawabi, Mataimakin gwamnan jihar Kebbi Alh.Samaila Yombe Dabai wanda Alh. Muhammed Kabiru Dabai (Yakaji) ya wakilta, ya bukaci jama’a su kaurace wa miyagun dabi’u kamar fashi da makami da kuma satar mutane, ya kuma ankarar da su muhimmancin zaben jam’iyar APC  a zabe mai zuwa.

Daga cikin wadanda suka yi jawabi a wajen taron akwai ACP Hayatu Usman wakilin Kwamishinan yansandan jihar Kebbi, Capt T.W Bawan wakilin C.O na Barikin Dakkarawa da ke Zuru, da wakilin Maimartaba Sarkin Zuru, hakazalika shugabannin al’umman Fulani na  kananan hukumomin  Danko Wasagu,  Fakai da kuma Sakaba duk sun yi jawabi ne kan muhimmancin tsaro .

Kafin a rufe taron, an raba goro bisa al’adar Fulani na rantsuwa irin ta Filato cewa za a kaurace wa ayyukan ashsha


DAGA ISYAKU.COM

Copyright, do not copy and paste our news on your blog without express written permission from us.

Shiga shafin mu na Facebook facebook.com/isyakuweb

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/AlFUDQouyehJRacXxBzbX0

Shiga cikakken shafin mu kai tsaye www.isyaku.com Tuntube mu ta SMS ko TEXT kawai zuwa 08087645001 ba mu amsa kira

WAYAR KA TA LALACE KO KANA BUKATAR FLASHING? 

Garzaya zuwa SENIORA TECH,shago mai lamba 50, hawa na sama gefen hagu,TAUSHI PLAZA , yamma daga gidan marigayi Waziri Umaru,kan Tiltin Ahmadu Bello, Nassarawa, Birnin kebbi jihar Kebbi. Barka da zuwa gidan sauki wajen gyaran wayar salula a garin Birnin kebbi.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN