Type Here to Get Search Results !

Atiku ya yi karin albashi ga ma'aikata 100.000 da ke aiki karkashinsa

Daga Legit Hausa

Dan takarar shugabancin kasa na jam'iyyar Peoples Democratic Party (PDP), Atiku Abubakar ya yiwa dukkan ma'aikatan da ke karkashinsa karin albashi zuwa N33,000.

Mohammed El-Yakub, Direktan Gotel Communications, kamfanin sadarwa mallakar Atiku da ke Yola ya tabbatarwa Sahara Reporters a yau Alhamis inda ya ce, "za a fara biyan sabuwar albashin mafi karanci na N33,000 daga watan Nuwamban 2018 kuma karin albashin ya shafi dukkan wadanda ke aiki karkashin Atiku har da masu hidima a gidajensa."

El-Yakub ya bayyana cewa a halin yanzu akwai kimanin mutane 100,000 da ke karbar albashi a kowanne wata a karkashin tsohon mataimakin shugaban kasar.Atiku ya yi kira ga shugaba Muhammadu Buhari ya amince da N30,000 a matsayin albashi mafi karanci kamar yadda kwamitin albashi da shugaban kasar ya kafa suka shawarci shi a cikin rahoton da suka gabatar masa.


DAGA ISYAKU.COM

Shiga shafin mu na Facebook facebook.com/isyakuweb

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/AlFUDQouyehJRacXxBzbX0

Shiga cikakken shafin mu kai tsaye www.isyaku.com Tuntube mu ta SMS ko TEXT kawai zuwa 08087645001 ba mu amsa kira

WAYAR KA TA LALACE KO KANA BUKATAR FLASHING? 

Garzaya zuwa SENIORA TECH,shago mai lamba 50, hawa na sama gefen hagu,TAUSHI PLAZA , yamma daga gidan marigayi Waziri Umaru,kan Tiltin Ahmadu Bello, Nassarawa, Birnin kebbi jihar Kebbi. Barka da zuwa gidan sauki wajen gyaran wayar salula a garin Birnin kebbi.

Post a Comment

0 Comments
* Please Don't Spam Here. All the Comments are Reviewed by Admin.

Top Post Ad

Below Post Ad

Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN