Atiku ya yi karin albashi ga ma'aikata 100.000 da ke aiki karkashinsa

Daga Legit Hausa

Dan takarar shugabancin kasa na jam'iyyar Peoples Democratic Party (PDP), Atiku Abubakar ya yiwa dukkan ma'aikatan da ke karkashinsa karin albashi zuwa N33,000.

Mohammed El-Yakub, Direktan Gotel Communications, kamfanin sadarwa mallakar Atiku da ke Yola ya tabbatarwa Sahara Reporters a yau Alhamis inda ya ce, "za a fara biyan sabuwar albashin mafi karanci na N33,000 daga watan Nuwamban 2018 kuma karin albashin ya shafi dukkan wadanda ke aiki karkashin Atiku har da masu hidima a gidajensa."

El-Yakub ya bayyana cewa a halin yanzu akwai kimanin mutane 100,000 da ke karbar albashi a kowanne wata a karkashin tsohon mataimakin shugaban kasar.Atiku ya yi kira ga shugaba Muhammadu Buhari ya amince da N30,000 a matsayin albashi mafi karanci kamar yadda kwamitin albashi da shugaban kasar ya kafa suka shawarci shi a cikin rahoton da suka gabatar masa.


DAGA ISYAKU.COM

Shiga shafin mu na Facebook facebook.com/isyakuweb

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/AlFUDQouyehJRacXxBzbX0

Shiga cikakken shafin mu kai tsaye www.isyaku.com Tuntube mu ta SMS ko TEXT kawai zuwa 08087645001 ba mu amsa kira

WAYAR KA TA LALACE KO KANA BUKATAR FLASHING? 

Garzaya zuwa SENIORA TECH,shago mai lamba 50, hawa na sama gefen hagu,TAUSHI PLAZA , yamma daga gidan marigayi Waziri Umaru,kan Tiltin Ahmadu Bello, Nassarawa, Birnin kebbi jihar Kebbi. Barka da zuwa gidan sauki wajen gyaran wayar salula a garin Birnin kebbi.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN