Muryar Amurka ta sallami ma'aikatan sashen Hausa 15 saboda karbar cin hanci


Muryar Amurka ta sallami ma’aikatan sashen Hausa 15, saboda zargin su da ake yi da rbar kudi da ya sabawa ka’idar aiki wato cin hanci. Daraktar Muryar Amurka Amanda Bennett ta bayyana ahakan a wani sakon imel da ta aikewa ma’aikata a ranar Alhamis, 4 ga watakn Oktoba.

Ta bayyana cewa cewa, an shaidawa hukumomin game da zargin su a cikin "watanni da suka gabata", nan da nan kuma aka kaddamar da bincike. Tace, “yayinda doka ta hanamu bada bayani daki-daki, bayan kammala binciken ne aka dauki matakin sallamar ma’aikatan.

" Amanda Bennett tace “wani gwamna ne daga daya daga cikin wadannan yankunan da Sashen Hausa ke watsa shirye-shiryensa, ya bada kudin.” Tace an kuma kaddamar da bincike domin tantance ko an watsa wadansu shirye shirye sabili da kudi da aka karba ne, kuma idan aka tarar da haka, za a dauki mataki nan take yadda ya kamata.

Bennet tace shugabannin sassan harsunan Afrika na Muryar Amurka sun bada cikakken goyon baya yayin gudanar da binciken da kuma shawarar da aka tsayar na sallama ko kuma niyyar sallamar wadanda abin ya shafa.
 

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/AlFUDQouyehJRacXxBzbX0 Shiga cikakken shafin mu kai tsaye www.isyaku.com Tuntube mu ta SMS ko TEXT kawai zuwa 08087645001 ba mu amsa kira

KANA ZAUNE A BIRNIN KEBBI? WAYAR KA TA LALACE KO KANA BUKATAR FLASHING? 

Garzaya zuwa SENIORA TECH,shago mai lamba 50, hawa na sama gefen hagu,TAUSHI PLAZA , yamma daga gidan marigayi Waziri Umaru,kan Tiltin Ahmadu Bello, Nassarawa, Birnin kebbi. Barka da zuwa gidan sauki wajen gyaran wayar salula a garin Birnin kebbi.

Hausa.naija.ng

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN