Type Here to Get Search Results !

Main event

'Yan bindiga sun sake yi wa mutane kisan kiyashi a Zamfara - Hotuna


'Yan bindiga sun kashe mutane 13 tare da raunata wasu da dama a wata hari da suka kai a kauyen Badarawa da ke karamar Shinkafi ta jihar Zamfara.

Daily Nigerian ta ruwaito cewa 'yan bindigan sun far ma kauyen ne da safiyar jiya yau Alhamis inda suka rika harbin dukkan wanda suka hadu dashi kuma daga baya suka rika bi gidajen mutane daukan abinda suke so.

Duk da cewa Rundunar 'yan sanda na jihar Zamfara ta ce mutane shida kawai aka kashe a harin, wata kwakwarar majiya daga kauyen ta ce mutane 13 ne suka rasu sakamakon harin.Kakakin Rundunar 'yan sandan jihar, Mohammad Shehu, ya tabbatar da afkuwar harin ga majiyar NAIJ.com amma ya ce mutane shida aka kashe a harin.

"Rahotannin da muka samu sun nuna cewa mutane shida aka kashe a harin, yayin da wasu 10 suka sami munanan raunuka. "Bayan an sanar da mu abinda ke faruwa, mun garzaya kauyen cikin gagagwa tare da sojojin Najeriya. Muna bin sahun 'yan bindigan a daji domin gano inda suke buya.

 "Mun baza jami'an sintiri a kauyen a yanzu kuma mutane sun fara cigaba da harkokinsu kamar yadda suka saba," inji mataimakin sufritanda, Shehu. Tuni dai aka yi jana'izar mutane da suka riga mu gidan gaskiya a harin na 'yan ta'adda.

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> whatsapp://chat?code=41x2TuRqdVQ9PrcrucqpTu Shiga cikakken shafin mu kai tsaye www.isyaku.com Tuntube mu ta SMS ko TEXT kawai zuwa 08087645001 ba mu amsa kira

Hausa.naij.ng

Post a Comment

0 Comments
* Please Don't Spam Here. All the Comments are Reviewed by Admin.

Top Post Ad

Below Post Ad

Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN

Hollywood Movies