'Yan bindiga sun sake yi wa mutane kisan kiyashi a Zamfara - Hotuna


'Yan bindiga sun kashe mutane 13 tare da raunata wasu da dama a wata hari da suka kai a kauyen Badarawa da ke karamar Shinkafi ta jihar Zamfara.

Daily Nigerian ta ruwaito cewa 'yan bindigan sun far ma kauyen ne da safiyar jiya yau Alhamis inda suka rika harbin dukkan wanda suka hadu dashi kuma daga baya suka rika bi gidajen mutane daukan abinda suke so.

Duk da cewa Rundunar 'yan sanda na jihar Zamfara ta ce mutane shida kawai aka kashe a harin, wata kwakwarar majiya daga kauyen ta ce mutane 13 ne suka rasu sakamakon harin.Kakakin Rundunar 'yan sandan jihar, Mohammad Shehu, ya tabbatar da afkuwar harin ga majiyar NAIJ.com amma ya ce mutane shida aka kashe a harin.

"Rahotannin da muka samu sun nuna cewa mutane shida aka kashe a harin, yayin da wasu 10 suka sami munanan raunuka. "Bayan an sanar da mu abinda ke faruwa, mun garzaya kauyen cikin gagagwa tare da sojojin Najeriya. Muna bin sahun 'yan bindigan a daji domin gano inda suke buya.

 "Mun baza jami'an sintiri a kauyen a yanzu kuma mutane sun fara cigaba da harkokinsu kamar yadda suka saba," inji mataimakin sufritanda, Shehu. Tuni dai aka yi jana'izar mutane da suka riga mu gidan gaskiya a harin na 'yan ta'adda.

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> whatsapp://chat?code=41x2TuRqdVQ9PrcrucqpTu Shiga cikakken shafin mu kai tsaye www.isyaku.com Tuntube mu ta SMS ko TEXT kawai zuwa 08087645001 ba mu amsa kira

Hausa.naij.ng

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN