Rahotanni sun kawo cewa kotun koli a kasar India ta halasta
yin luwadi da madigo a kasar, matakin da aka dade wasu na adawa da shi. Kotun
ta halatta yin hakan ne ga manya da suka mallaki shekarun girma.
Hukuncin dai ya yi wa
masu gwagwarmayar kare 'yan luwadi da madigo dadi inda suka rungume juna suna
murna bayan yanke hukunci da kotun tayi. Alkalai biyar ne suka yi nazari akan
hukuncin da aka yanke a shekara ta 2013.
Tsohuwar dokar tun zamanin turawan mulkin mallaka da aka fi
sani da sashe na 3-7-7 ta zartar da hukuncin duk wanda aka samu da yin madigo
da luwadi za a yanke masa hukuncin ko dai sama da shekara 10 a gidan kurkuku.
Tun da farko ma su fafutuka sun ce ayyana auren jinsi a
matsayin laifi, zai zama babbar barazana ga 'yancin masu ra'ayin auren jinisi
daya. A baya NAIJ.com ta rahoto cewa Allah madaukakin sarki ya tona asirin wani
hamshakin dan kasuwan jihar Kano da ya shahara wajen aikata luwadi da kananan
Yara.
Majiyarmu ta ruwaito
a ranar Laraba 25 ga watan Yuli ne wata Kotun majistri dake jihar Kano ta aika
da wannan attajiri, Balarabe Habibu zuwa gidan Yari sakamakon zarginsa da ake
yi da yin luwadi da wani yaro mai shekara Tara.
Dansanda mai shigar da kara, Sufeta Pogu Lale ya shaida ma
Kotun cewa Habibu mai shekaru 41 mazauni a unguwar Dullurawa ya aikata luwadi,
wanda hakan ya saba ma sashi na 284 na kundin hukunta manyan laifuka.
Dansandan yace mahaifin wannan yaro mai suna Muratala Sa’idu
tare da mahaifiyarsa Aisha Khalid ne suka kai karar wannan mutumi zuwa ofishin
Yansanda dake Jakara a ranar 6 ga watan Yuli.
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> whatsapp://chat?code=41x2TuRqdVQ9PrcrucqpTu Shiga cikakken shafin mu kai tsaye www.isyaku.com Tuntube mu ta SMS ko TEXT kawai zuwa 08087645001 ba mu amsa kira
Hausa.naij.ng