Hakkin yan Pansho ya makale a hannun Gwamnatin jihar Kebbi, sun koka a biyasu

Isyaku Garba | 16-9-2018 |
Tsofaffin ma'aikatan gwamnatin jihar Kebbi sun sake kokawa akan rashin biyansu hakkokinsu na Gratuti da Pansho. A yan makonnin baya ne kungiyar tsofaffin ma'aikatan na jihar Kebbi Retired Officers Welfare Association ROWA, ta kira wani taro na yayanta daga ko'ina a fadin jihar inda ta yi yunkurin gudanar da addu'a a babban Masallacin idi na garin Birnin kebbi domin neman Allah ya saka masu sakamakon rashin biyansu hakkinsu. Amma daga bisani aka shiga tsakanin yayan kungiyar da gwamnatin jihar Kebbi.

A halin yanzu dai, gwamnatin jihar Kebbi ta kasa biyan wadannan kudaden, wanda sakamakon haka ya ci gaba ada haifar da matsanancin halin kuncin rayuwa ga wadannan bayin Allah da suka bauta ma gwamnatin jihar Kebbi har tsawon shekaru masu yawa, amma daga karshe sai ga gwamnatin APC karkashin jagorancin Gwamna Atiku Bagudu tana tafiyar hawainiya wajen ganin ta biya wadannan bayin Allah hakkokinsu.

Saurari Alh,.Babangida Garba Gwandu (Danburam)👇



Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/AlFUDQouyehJRacXxBzbX0 Shiga cikakken shafin mu kai tsaye www.isyaku.com Tuntube mu ta SMS ko TEXT kawai zuwa 08087645001 ba mu amsa kira

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN