Yayin da zabukan gama-gari na shekarar 2019 ke kara matsowa,
kusan a iya cewa duk wani dan siyasa yanzu hankalin sa ya karkata ne a can
bangaren.Kamar dai yadda aka zata, masana harkokin siyasa da masu sharhi akan
al'amurran yau da kullum a ko da yaushe sukan dauki lokaci suna bincike sannan
kuma su bayyanawa jama'a yadda suke hasashen zabukan za su kasance.
NAIJ.com ma a nan ta danyi bincike akan wasu dalilan da ka
iya sa shugaba Muhammadu Buhari ya fadi zaben 2019 idan har ba'a yi gyara ba.
1. Rashin adalci wajen nade-naden mukamai Masu sharhi akan
al'amurran siyasa a kasar nan dai na ganin dole ne shugaban kasa Muhammadu
Buhari ya sake yin duba akan yadd yake yin nade-naden sa saboda al'ummar
kudancin kasar na zargin ba yayi masu adalci. Duk da dai shugaban kasar ya sha
karyata hakan.
2. Yiwuwar sasanci a tsakanin 'yan takarar adawa Haka ma dai
ana ganin idan har 'yan adawa musamman ma na jam'iyyar PDP dake neman tikitin
yin takarar da Shugaba Buhari a 2019 suka hada kan su suka fitar da mutum daya
kwakkwara, to lallai za su iya kayar da shi.
3. Rarrabuwar kuri'un yankin Arewa Kowa yasan da yawa daga
magoya bayan shugaba Muhammadu Buhari, duk daga yankin arewacin kasar nan suke.
To ana ganin idan har jam'iyyun adawa suka raba kawunan 'yan arewar musamman ma
wajen kuri'un su, to tabbas za su iya kada shi a zaben.
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/AlFUDQouyehJRacXxBzbX0 Shiga cikakken shafin mu kai tsaye www.isyaku.com Tuntube mu ta SMS ko TEXT kawai zuwa 08087645001 ba mu amsa kira
Hausa.naij.ng
Tags:
LABARI