Barazan kan rayuwar Atiku: PDP ta yiwa APC gugar zana


A cikin satin da muka yi bankwana da shi ne tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya koka kan cewar ana yiwa rayuwarsa da ta iyalinsa barazana saboda burinsa na son yin takarar shugaban kasa a zaben 2019.

Sai dai jam’iyyar adawa ta PDP ta ce babu wanda zata yi zargi idan ba jam’iyyar APC ba matukar wani abu ya samu daya daga cikin ‘yan takarar ta. A jawabin da PDP ta fitar ta bakin Kola ologbondian, sakataren yada labarai na jam’iyyar, ta ce ba zata taba daukan batun barazana kan rayuwar Atiku da wasa ba tare da yin kira ga shugaba Buhari day a bayar da umarnin gudanar da bincike a kan dukkan koarfe-korafen da Atiku ya aike masa a rubuce.

 Ologbondian ya bayyana cewar tuni jam’iyyar APC ta shiga halin dimuwa da damuwa saboda irin nagartar ‘yan takarar shugaban kasa da PDP ke da su tare da zargin gwamnati da yin amfani da ‘yan banga da jami’an tsaro domin kuntatawa ‘yan takarar ta.

“Tun da jam’iyyar APC ta fahimci cewar dukkan ‘yan takarar mu sun fi karfin Buhari suka fara amfani da karnukan farauta a cikin hukumomin tsaro na gwamnati musamman ‘yan sanda, jami’an DSS da na hukumar EFCC domin firgita ‘yan takarar mu dake son yin takara a zaben 2019. “Yanzu lamarin ya wuce amfani da karfin gwamnati har ya kai ga yin barazana a kan rayuwar ‘yan takarar mu. Muna son sanar da APC cewar babu abinda zai firgita mu ko ya saka tsoro a zukatanmu,” a cewar Ologbondian. 

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/AlFUDQouyehJRacXxBzbX0 Shiga cikakken shafin mu kai tsaye www.isyaku.com Tuntube mu ta SMS ko TEXT kawai zuwa 08087645001 ba mu amsa kira

Hausa.naij.ng

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN