Type Here to Get Search Results !

Banbancin siyasa: Wani Gwamna ya sallami manyan Hadimansa 28 a rana daya


Zaku ji cewa tsananin adawa dake tattare cikin siyasa musamman ta kasar nan ta sanya gwamnan jihar Benuwe, Samuel Ortom, ya fatattaki hadiman gwamnatin sa kimanin 28 kamar yadda rahotanni da sanadin shafin jaridar The Nation suka bayyana. Rahotannin sun bayyana cewa, gwamnan ya sallami hadiman sa na musamman guda 17, yayin ya yiwa manyan hadiman sa 11 sallama ta 'Umma ta gaida Assha' cikin ruwan sanyi domin yiwa gwamnatin sa garambawul da sauya fasalin 'yan majalisa da makarrabansa.

Sakataren gwamnatin jihar, Tony Ijoho, shine ya bayar da sanarwa yanke alakar hadiman 28 da kuma gwamnan jihar, inda ya neme su akan mika dukkanin wani mallaki na gwamnatin a hannun sakatarorin su na dindindin. Binciken manema labarai ya bayyana cewa, gwamnatin jihar ta raba gari da hadimanta ne domin bai wa sabbi dama ta maye guraben su musamman 'yan jam'iyyar adawa ta PDP.

NAIJ.com ta fahimci cewa, gwamna Ortom ya karbi ragamar gudanar da al'ummar jam'iyyar PDP tun yayin da ya sauya sheka ta ficewa daga jam'iyyar APC. Gwamnan yana daya daga cikin jiga-jigan kasar nan da guguwar sauyin sheka ta kada su yayin da suka yi hannun riga da jam'iyyar ta APC makonni kadan da suka gabata.
 

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> whatsapp://chat?code=41x2TuRqdVQ9PrcrucqpTu Shiga cikakken shafin mu kai tsaye www.isyaku.com Tuntube mu ta SMS ko TEXT kawai zuwa 08087645001 ba mu amsa kira

Hausa.naij.ng

Top Post Ad

Below Post Ad

Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN