An tsinci gawar Manjo Janar Idris Alkali -sojan Najeriya da ya bace kwanakin baya


Labarin da muke samu daga majiyoyin mu dai na nuni ne da cewa babban jami'in sojan Najeriyar nan watau Manjo Janar Idris Alkali da muka baku labarin bacewar sa a kwanan baya an tsinci gawar sa.

 Mun samu cewa dai an tsinci gawar sojan ne a garin Jos ta jihar Filato a kusa da asibitin koyarwa ta jami'ar tarayya dake jihar akan hanyar zuwa matsugunnin jami'ar na din din din. NAIJ.com dai ta samu cewa jami'an tsaron Najeriya ne suka gano gawar ta sa tare da wasu masu sana'ar adai-daita a cikin wani kududdufi dake a garin.

Haka zalika dai majiyar tamu tace ana kyautata zaton 'yan kabilar Birom ne dake a jihar suka kashe su duk da yake dai har yanzu ba samu wani bayani ba daga hukumar sojin kasar game da lamarin. A wani labarin kuma, Yayin da zabukan shekarar 2019 ke ta kara karatowa, wasu masoyan dan takarar shugabancin kasar dake neman tikitin tsayawa a jam'iyyar adawa ta PDP, Dakta Rabi'u Musa Kwankwaso sun yanka rago tare da addu'o'i ga Allah akan muradin na su.

Kamar yadda muka samu, masoyan na Kwankwaso da galibin su matasa ne sun fito ne daga karamar hukumar Kiru dake a jihar Kano inda kuma suka gudanar da Sallah da saukar al'qur'ani duk domin samun nasarar gwanin nasu.
 
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/AlFUDQouyehJRacXxBzbX0 Shiga cikakken shafin mu kai tsaye www.isyaku.com Tuntube mu ta SMS ko TEXT kawai zuwa 08087645001 ba mu amsa kira

Hausa.naij.ng

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN