Kotu ta yiwa babban sufetan ‘yan sanda albishir da tura shi gidan yari

Wata babbar kotu dake zamanta a Ilorin, babban birnin jihar Kwara, karkashin mai shari’a, Ibrahim Yusuf, tayi barazanar tisa keyar babban sifetan hukumar ,yan sandan Najeriya, Idris Ibrahim, zuwa gidan yari saboda raina umarninta.

Kotun na zargin Idris da raina umarninta na sakin Mista Olalekan Alabi, wani mataimaki na musamman a kan harkokin siyasa ga gwamnan jihar Kwara, Abdulfatah Ahmed.

Barazanbar tura Sufeto Idris gidan yarin na kunshe ne cikin wata takardar jan kunne mai lamba ta 48 da kotun ta buga a ranar 10 ga watan Agusta. Takardar da aka raba ga manema labarai yau, Alhamis, a Ilorin ga manema labarai na dauke da saka hannun rajistaran kotun.

A cikin takardar, a lkalin kotun, Yusuf, ya ce “ka sani cewar matukar baka yi biyayya ga umarnin babbar kotu dake jihar Kwara ba a kan hukuncin da ta yanke ranar 1 ga watan Agusta, 2018, ba tamkar nuna raini ga bangaren shari’a ne wanda hukuncinsa shine tisa keyar ka zuwa gidan yari.”

Hukumar ‘yan sanda ta kama tare da tsare Alabi ne tun ranar 30 ga watan Mayu bayan an yi zarginsa da alaka mai karfi da ‘yan fashin garin Offa. Sai dai mai shari’a Yusuf ya bayar da umarnin a saki Alabi a kan beli na wucin gadi a ranar 1 ga watan Agusta tare da bayyana cewar babu hujjar cigaba da tsare shi.
 

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> whatsapp://chat?code=41x2TuRqdVQ9PrcrucqpTu Shiga cikakken shafin mu kai tsaye www.isyaku.com Tuntube mu ta SMS ko TEXT kawai zuwa 08087645001 ba mu amsa kira
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN