Rahotanni sun fallasa kasar Iran a matsayin kasar dake
taimaka ma yan Shi’a da makamai don sun kaddamar da yaki a kasar Iraqi da
sauran kasashen dake hamayya dasu, inji rahoton jaridar Daily Trust.
Majiyar NAIJ.com ta ruwaito kasar Iran na cigaba da karfafa
mayakan yan shia dake kasar Iraqi mai suna Quds da makaman kare dangi watau
nukiliya don su kare kansu tare da kai ma duk wata kasar dake yaki dasu hari.
Wani hadakar jami’an gwamnatin kasar Iran guda uku, jami’a
leken asiri na kasar Iraqi da wasu jami’an kasashen turai ne ta bayyana haka,
inda tace a yanzu haka Iran ta aika da makaman nukiliya masu kananan zango ga
yan shi’ar kasar Iraqi a watannin da suka gabata.
Haka zalika wasu jami’an leken asiri guda biyar sun tabbatar
da cewar Iran na taimaka ma yan shi’an Iraqi da kayan aiki domin su fara kera
makamansu da kansu. “Hikimar yin haka shine don Iran ta samu tufun dafawa idan
har an kai mata hari. “Nukilyan da ta baiwa yan shi’an basu dayawa, basu wuce
dozin daya ba, amma zasu iya kara yawansu idan bukatar haka ya taso.”
Inji wani jami’in kasar Iran. A baya kasar Iran ta sha yin
ikirarin cewa makaman nukiliya da take kerawa zata yi amfani dasu ne kawai idan
an tabata, amma sai ga shi da aka tambayi manyan jami’an kasar game da wannan
batu sai suka zuke, suka ki cewa uffan.
Daga cikin makaman da yan shi’an kasar Iraqi suka samu akwai
wasu nukiliyoyi masu suna Zelzal, Fateh-110, da Zolfaqar wanda zasu iya kai
nisan kilomita 200 zuwa 700, wanda hakan ya sanya kasashen adawar Iran
Isara’ila da Saudiyya cikin wannan zango.
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> whatsapp://chat?code=41x2TuRqdVQ9PrcrucqpTu Shiga cikakken shafin mu kai tsaye www.isyaku.com Tuntube mu ta SMS ko TEXT kawai zuwa 08087645001 ba mu amsa kira
Hausa.naij.ng
Tags:
LABARI