Grema Terrab, wani dan siyasa kuma mai takarar kujerar
gwamna a jihar Borno, ya fada komar ‘yan sanda a yau, Talata, bayan hukumar ta
dade da bayyana nemansa ruwa a jallo. Jami’an SARS ne suka kama Terrab a wurin
wani taron da Atiku Abubakar ya halarta.
Hukumar ‘yan sanda ta ayyana neman Terrab ruwa a jallo bisa
zarginsa da taka rawa a wani laifin kisa da aka yi a wurin wani taron siyasa da
aka yi a gidansa tun watan Afrilu. A yau ne Mista Terrab ya bayyana a garin
Maiduguri tun bayan day a bar garin a watan na Afrilu. Rahotanni sun bayyana
cewar Mista Terrab ne da kansa ya sanar da hukumar ‘yan sanda batun kisan, amma
duk da haka saida jami’an ‘yan sandan suka kama matar sa tare da tsar eta na
tsawon sati biyu. Lamarin day a yi sanadiyar zubewar juna biyu da take dauke da
shi .
Fastoci da allunan tallar Mista Terrab a matsayin dan
takarar gwamnan jihar Borno a karkashin jam’iyyar PDP sun shiga kowanne lungu
da sako na garin Maiduguri. Bayan samun rahotannin zuwansa wurin taron, sai
jami’an ‘yan sanda sun yiwa wurin kawanya kuma da bayyanarsa keda wuya suka
cika hannu da shi.
Kokarin Mista Terrab na jan hankalin Atiku domin ya cece shi
bai samu cika yayinda jami’an tsaron Atikun suka fita da shi daga wurin taron.
An hangi Mista Terrab na rike gefen babbar rigar Atiku domin ya hana a tafi da
shi. Kazalika duk rokon yaransa domin jami’an ‘yan sandan su sake shi bai samu
karbuwa ba.
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/Lq4Z5kPck53Le3ibU9RUnY Latsa nan domin ka sauke Manhajarmu ISYAKU.APK https://docs.google.com/uc?export=download&id=0B7lmLLhGZSx5OTVENFlsTkllRTQ Shiga cikakken shafin mu kai tsaye www.isyaku.com Tuntube mu ta SMS ko TEXT kawai zuwa 08087645001 ba mu amsa kira
Hausa.naij.ng