An sha yin tambayar shin zai yiwu kuwa samari da 'yan mata suyi soyayya babu karya a ciki amma sai dai amsar da take biyo har yau bata gamsar ba Yanzu dai ƙarya ta zama ruwan dare a soyayya tsakanin samari da yan mata, sai dai akwai wasu ƙaryayyaki da suka fi shahara a bangaren samari, hakan ba yana nufin yan matan ba sa yin karya ba, su ma da akwai nasu irin salon ƙaryar, sai dai a nan za a yi duba ne akan wasu kadan da samari ke shararawa yan matan.
1- Ke kaɗai nake muradi a rayuwa: Sau da yawa zaka ji samari
na fadawa mace cewa ita kadai suke muradi a rayuwa, amma da zaka yi duba sosai
akan wanda ya furta wannan lafazi zaka same shi da jerin-gwanon yan mata
daban-daban wanda suma hakan yake fada musu. Kadan ne cikin samari zaka same su
wanda in har suka furta hakan yake tabbas daga zuciyar su.
2- Ke kaɗai ce, bani da Budurwa Wannan ma wani salon karya,
sau da dama zaka riske saurayi ya fadawa budurwa haka ne saboda ya samu karbuwa
a wajenta, amma maganar gaskiya ba haka zancen yake ba, saboda zaka iya samun
sa da yan mata da yawa a lokaci daya. Wannan salo na karya shi ma ya yi fice a
tsakanin samari da yan matan baki daya.
3- Gaba daya dangi na sun san da zamanki Allah sarki yan
mata, saurayi sai ya dage ya shararo miki karyar cewa danginsa da mahaifiyarsa
ta san dake a matsayin wadda yake so. In har haka ne abinda ya fada ya kamata
ace ko sau daya ne ya kai ki wajen mahaifiyar tasa kun gaisa ko kuma ya hada ku
ta waya kuke gaisawa ko kuma ya hada ki da 'yan uwansa kuke yin zumunci wanda
hakan ne zai tabbatar miki da gaskiyar abinda yake fada.
4- Abokiyar aiki na ce Zaki iya samun saurayi tare da wata
daban amma idan kin yi magana sai ya ce miki abokiyar aikinsa ce, ma'ana suna
aiki tare ne a wajen aikinsa, amma da zaki yi bincike na tsanaki zaki riske
cewar budurwarsa ce. Wannan nau'i na karya shi ma ya yi shuhura sosai a
tsakanin samari.
5- Ke kaɗai ce a rayuwata Allah ya tsari gatari da saran
shuka, ya kamata dai samari su rage yiwa yan mata karya, dalili kuwa a nan shi
ne duk saurayi da ya fada miki haka, to, tabbas ki sake tamabayar sa shin hakan
da gaske domin ki samu tabbaci. Don da yawansu zasu fada miki haka amma zaki
same shi ba wai ke kadai yake soyayya dake ba watakila ma har ƙawarki ko
aminiyarki yake soyayya da ita ba tare da sanin ki ba.
Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com
hausa.naij.ng