Gwamna Bagudu zai sake tsayawa takara ne da Samaila Yombe a 2019 - Faruku Inabo

Mai taimaka wa Gwamna Abubakar Atiku Bagudu a ayyuka na Musamman watu P.A Faruku Inabo ya tabatar wa mutanen Masarautar Zuru cewa Gwamna Bagudu zai tsaya takara ne tare da Mataimakinsa Alh. Samaila Yombe Dabai a shekara ta 2019. Ya ce babu wata matsala tsakanin Gwamna Atiku Bagudu da Mataimakinsa Samaila Yombe sai alhairi da mutunci. Ya kuma bukaci jama'ar ta kasar Zuru su guje wa jita-jita ko wasu kananan maganganu.

Alh. Faruku Inabo ya yi wannan jawabin ne a gidan Mataimakin Gwamna yayin da ya je domin ya yi wa jama'ar kasar Zuru da suka zo  Birnin kebbi domin taron APC na jihar Kebbi godiya. Motoci fiye da 20 ne suka yi jerin gwano daga Zuru zuwa Birnin kebbi dauke da jama'a domin taron.

Alh. Nura Mai Fata ,wanda shi ne mataimakin shuga na kungiyar 4+4 mai fafutukar ganin cewa Gwamna Atiku Bagudu ya sake tsayawa takara a 2019 ya ce sun zo ne domin su amsa gayyatar uwar kungiya ta APC haka zalika domin su tattauna bisa wasu lamaura da Mataimakin Gwamana dangane da Masarautar Zuru.

Tuntube mu ko aiko Labari zuwa isyakulabari@gmail.com Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com *** GURBIN TALLA *** Kana son ka yi flashing ko ka cire makulli watau security na wayar ka? ka zo SENIORA TECH a OLUMBO PLAZA yamma da Gidan Wazirin Gwandu kan titin Ahmadu Bello a garin Birnin Kebbi. Shago Lamba 51 hawa na sama.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN