Bisa al'adar al'umman garin, Shu'aibu ya gaji Satina bayan rasuwar yayansa kuma an gudanar da tsare-tsare na gargajiya a watan Fabrairu na bana sai suka tare suka fara zama tare a kauyen Kuruduma II a Asokoro na babban birnin tarayya Abuja.
Kwamishinan 'yansanda na birnin tarayya Muhammed Saddik Bello ya ce Shu'aibu ya sami labari cewa Satina tana nema da wani, amma marmakin Shu'aibu ya yi bincike sai ya kashe ta.
Ganin tsananin laifin da ya aikata, Shu'aibu ya ruga zuwa cikin kichin ya bulbula wa jikinsa kalanzir ya kyasta wa kanshi wuta daga bisani kuma ya kai kanshi wajen 'yansanda a chaji Ofis na Asokoro.
Shu'aibu ya shaida wa Manema labarai cewa aikin shedan ne, domin ya san ya aikata abin da bai kamata ba.Ya kuma roki iyalinsa da Iyayen Satina su yafe masa domin ya san ya yi kuskure.
.
**************************************** Tuntube mu ko aiko Labari zuwa isyakulabari@gmail.com Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com **************************************** Kana son ka yi flashing ko ka cire makulli watau security na wayar ka? ka zo SENIORA TECH a OLUMBO PLAZA yamma da Gidan Wazirin Gwandu kan titin Ahmadu Bello a garin Birnin Kebbi. Shago Lamba 51 hawa na sama.
Hoto: sunnewsonline