An kona rabin kasuwar Bwari sakamakon rikicin kabilanci a Abuja

Bayanai da ke fitowa daga birnin Abuja sun nuna cewa an sami barkewar rikici mai nasaba da kabilanci a garin Bwari tsakanin 'yan kabilar Gbagi da kuma  Hausawa wanda hakan ya yi sanadin kone kusan rabin kasuwar ta Bwari.

Rahotanni sun nuna cewa rigamar ta samo asali ne tun ranar daren Lahadi bayan an zargin cewa wasu 'yan kungiyar asiri sun kashe wani mutum a garin wanda ya haifar da 'yar hatsaniya da ya lafa .

BBC ta ruwaito cewa kwatsam da sanyin safiyar Litinin sai kurar rikocin ta sake tashi wanda ya kai ga baza jami'an 'yansanda a garin na Bwari.

Kawo yanzu dai ba'a san ko mutum nawa ne suka mutu ba haka zalika babu kididdiga akan yawan dukiya da ya salwanta.

Tuntube mu ko aiko Labari zuwa isyakulabari@gmail.com Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com *** GURBIN TALLA *** Kana son ka yi flashing ko ka cire makulli watau security na wayar ka? ka zo SENIORA TECH a OLUMBO PLAZA yamma da Gidan Wazirin Gwandu kan titin Ahmadu Bello a garin Birnin Kebbi. Shago Lamba 51 hawa na sama.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN