4+4 a Masarautar Zuru ta dau himma, shugabanni sun kawo ziyara B-kebbi

Shugabannin hadaddiyar kungiyar 4+4 na Masarautar Zuru sun kai ziyarar godiya ga Mataimakin Gwamnan jihar Kebbi Alh. Samaila Yombe Dabai a gidansa da ke Birnin kebbi domin nuna godiya bisa amana da aka damka masu.

Jagoran ziyarar kuma mataimakin shugaban tafiyar 4+4 na jihar Kebbi Alh. Nura Mai Fata ya shaida wa ISYAKU.COM cewa manufar ziyarar tasu shine domin su kara jaddada godiya bisa amana da aka damka masu kuma su yi amfani da damar domin tuntuban Mataimakin Gwamna akan wasu tsare-tsare domin ganin an sami nassara a sha'anin 4+4 a Masarautar Zuru.

Daga cikin shugabannin 4+4 na Masarautar Zuru da ke cikin tawagar sun hada da Alh. Nura Mai Fata Mataimakin Chairman 4+4 na jiha, Alh. Muhammadu Dan Tata Dirin daji Chairman 4+4 Sakaba L.govt., Alh. Inuwa Mai Attah Chairman 4+4 Zuru L.govt, Alh Dauda Aliyu Bena Chairman 4+4 Danko-Wasagu L.govt da Alh. Aliyu Muhammed Atapha Chairman 4+4  Sakai L.govt.

Tuntube mu ko aiko Labari zuwa isyakulabari@gmail.com Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com *** GURBIN TALLA *** Kana son ka yi flashing ko ka cire makulli watau security na wayar ka? ka zo SENIORA TECH a OLUMBO PLAZA yamma da Gidan Wazirin Gwandu kan titin Ahmadu Bello a garin Birnin Kebbi. Shago Lamba 51 hawa na sama.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN