Yadda aka gudanar da taron al'umman kasar Zuru mazauna jihar Kebbi

Mataimakin Gwamnan jihar Kebbi Alh. Samaila Yombe Dabai ya yi kira ga al'uman kasar Zuru mazauna jihar Kebbi su hada kansu ya kasance tsintsiya madaurin ki daya. Yombe ya yi wannan kiran ne yayin da yake jawabi a wajen taron al'umman kasar Zuru a dakin taro na CST Polytechnic Birnin Kebbi .

Ya kara da cewa zumunci abu ne mai muhimmancin gaske ganin cewa duk abu daya ne tsakanin 'dan Zuru da 'dan Zuru ko 'yar Zuru.

Yombe ya kuma yi kira ga duk 'dan kasar Zuru da cewa ya taimake 'danuwansa a duk inda ya sami kanshi haka zalika ya ce shirya irin wannan taron yana da muhimmanci ganin cewa zai kara dankon zumunci da fahimtar juna a tsakanin 'yan kasar ta Zuru.

Taron ya sami halarcin 'yan asalin kasar Zuru kamar su Rector na Makarantar Koyon Fasaha ta Waziri Umaru da ke Birnin kebbi, Malam Sani, Hajiya Maimuna M. Bala ,tsohon  G. M kebbi Radio Alh.Bello Ibrahim  Ribah hadi da S.A Abdul-rahaman Manga  da dai sauransu. Alh. Isah Abdullahi, 

Tuntube mu ko aiko Labari zuwa isyakulabari@gmail.com Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN