Mataimakin Gwamnan jihar Kebbi Alh. Samaila Yombe Dabai ya yi kira ga al'uman kasar Zuru mazauna jihar Kebbi su hada kansu ya kasance tsintsiya madaurin ki daya. Yombe ya yi wannan kiran ne yayin da yake jawabi a wajen taron al'umman kasar Zuru a dakin taro na CST Polytechnic Birnin Kebbi .
Ya kara da cewa zumunci abu ne mai muhimmancin gaske ganin cewa duk abu daya ne tsakanin 'dan Zuru da 'dan Zuru ko 'yar Zuru.
Yombe ya kuma yi kira ga duk 'dan kasar Zuru da cewa ya taimake 'danuwansa a duk inda ya sami kanshi haka zalika ya ce shirya irin wannan taron yana da muhimmanci ganin cewa zai kara dankon zumunci da fahimtar juna a tsakanin 'yan kasar ta Zuru.
Taron ya sami halarcin 'yan asalin kasar Zuru kamar su Rector na Makarantar Koyon Fasaha ta Waziri Umaru da ke Birnin kebbi, Malam Sani, Hajiya Maimuna M. Bala ,tsohon
G. M kebbi Radio Alh.Bello Ibrahim Ribah hadi da S.A Abdul-rahaman
Manga da dai sauransu. Alh. Isah Abdullahi,