Rahotanni daga kasar Zimbabwe sun nuna cewa Sojin kasar sun kifar da Gwamnatin shugaba Robert Mugabe na jam'iyar Zanu PF a daren Talata bayan an ji karar fashe-fashen ababe da ake dangantawa da igwa kuma daga bisani aka ji karan harbin bindigogi a Harare babban birnin kasar.
Shugaban kasar Afrika ta kudu Jecob Zuma ya ce shugaba Robert Mugabe ya shaida masa ta wayar tarho cewa yana tsare a gidansa kuma yana cikin koshin lafiya.
Wata majiya ta labarta cewa Mugabe ya bukaci a bar Matarsa Grace ta fice lafiya kalau zuwa kasar Afrika ta kudu.Wannan juyin mulkin Soja shi ya kawo kashen mulkin shugaba Robert Mugabe na tsawon shekara 37 a kasar.
Mr Jecob Zuma na Africa ta kudu ya bukaci a kwantar da hankali kuma a kai zuciya nesa a kasar ta Zimbabwe kuma ya bukaci rundunar Sojin kasar su bi a sannu.
Tuntube mu ko aiko Labari zuwa isyakulabari@gmail.com Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com
Shugaban kasar Afrika ta kudu Jecob Zuma ya ce shugaba Robert Mugabe ya shaida masa ta wayar tarho cewa yana tsare a gidansa kuma yana cikin koshin lafiya.
Wata majiya ta labarta cewa Mugabe ya bukaci a bar Matarsa Grace ta fice lafiya kalau zuwa kasar Afrika ta kudu.Wannan juyin mulkin Soja shi ya kawo kashen mulkin shugaba Robert Mugabe na tsawon shekara 37 a kasar.
Mr Jecob Zuma na Africa ta kudu ya bukaci a kwantar da hankali kuma a kai zuciya nesa a kasar ta Zimbabwe kuma ya bukaci rundunar Sojin kasar su bi a sannu.
Tuntube mu ko aiko Labari zuwa isyakulabari@gmail.com Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com
Tags:
LABARI