Daga Nura Bena, Isyaku Garba |
An bayyana mai girma mataimakin Gwamnan jihar kebbi, Alh.
Samaila Yombe Dabai, a matsayin hazikin Soja gwarzon na miji da bai da
tsoro.
Wannan yabon ya fito ne daga wasu Manya sojoji da kuma
abokan sa a lokacin da suka halarci shedar baikon 'ya 'yan shi biyu da
za a gudanar da daurin aurensu kwanan nan.
'Ya 'yan dai na mataimakin Gwamnan jihar kebbi , Sun
had da Rakiyya Samaila Yombe Dabai, da Basira Samaila Yombe Dabai.
Tambayar auren an gudanar da shi ne a Gidan mai Mataimakin Gwamnan, jihar kebbi Alh. Samaila yombe Dabai, a unguwar
kurmin Mashi da ke jihar kaduna.
Da yeke amincewa a madadin Mataimakin Gwamnan ,
watau Wakilin Zurun Kaduna da kewaye, Alh. Zubairu Kabiru Danjuma, ya
ce ya aminta da bada su baiko tare da yanka masu sadaki kamar yadda
addinin Musulunci ya tanada, tare da yi masu fatan Alkhairi.
Ya kara da cewa ana sa ran gudanar da Daurin Auren a watan gobe watau Disamba in Allah ya kai mu.
A jawabin sa jim kadan bayan kammala tambayar Auren, Mataimakin Gwamnan jihar Kebbi Alh. Samaila Yombe Dabai ya gode wa dukkanin wadanda suka halarci gudanar da lamarin, tare da fatan alkhairi ga duk wanda ke da hannu ganin an samu nassarar hakan.
A jawabin sa jim kadan bayan kammala tambayar Auren, Mataimakin Gwamnan jihar Kebbi Alh. Samaila Yombe Dabai ya gode wa dukkanin wadanda suka halarci gudanar da lamarin, tare da fatan alkhairi ga duk wanda ke da hannu ganin an samu nassarar hakan.
Alh. Samaila Yombe Dabai ya kara yana bayyana aure a
mastayin daya daga cikin Sunnan Manzon tsira, tare da yin kira ga ci gaba
da yin koyi da Manzo (SAW) hadi da yin hakuri da junan su, ganin cewa
aure fa ba abin wasa bane.
Mataimakin Gwamnan na kebbi ya gode wa Gwamnan jihar Kebbi Sanata Abubakar Atiku Bagudu akan irin shawara , da kuma goyon bayan sa a kowa ne lokaci, tare da dukkanin jama'ar Jihar kebbi baki daya.
Haka zalika daga cikin wada da suka amsa tabayoyin manema labairai a wurin akwai manyan sojin kasarnan wadan da suka bayyana, Kanal (Col.) Samaila Yombe Dabai, a matsayin haziki kuma jarumi, a duk inda yake, ba raggo ba ne, na mijin gaske ne, shi ya sa a duk lokacin da lamarinsa ya tashi dole ne su mara masa baya.
Sun Kara da cewa Jihar Kebbi ta yi sa'a da samun gwarzo kuma kwararren Gwamna Sanata Abubakar Atiku Bagudu (Matawallen Gwandu)
tare da samun haziki kuma Jarumin mataimakin Gwamna col. Samaila Yombe Dabai
mni,(Tambarin Zuru kuma Turakin Dabai).
Sauran wadanda suka yi jawabi a wurin sun hada da Wakilin
Zurun kaduna da Kuma Shugaban karamar hukumar mulki ta Yauri Alh. Musa
stone hadi da Alh. Dan musa Ribah dukkaninsu sun nuna jin dadin su akan sha 'anin bada auren.
Haka Kuma sun shawarci ma auratan da su yi hakuri da junan su da fatan Allah yasa wa auren da za ayi Albarka.
Haka Kuma sun shawarci ma auratan da su yi hakuri da junan su da fatan Allah yasa wa auren da za ayi Albarka.
Cikin wadanda suka samu halarci lamarin sun hada da manya tsoffin Soji na sama da na kasa a ciki da wajen kasarnan.
Sauran mahalarta sun hada da wasu manya daga Majalisar dinkin Duniya UN da na DAFUR hadi da na hukumar Dept.of Safety and Sec. Abuja da maiduguri.
Sauran mahalarta sun hada da wasu manya daga Majalisar dinkin Duniya UN da na DAFUR hadi da na hukumar Dept.of Safety and Sec. Abuja da maiduguri.
Tuntube mu ko aiko Labari zuwa isyakulabari@gmail.com Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com